Na Ɗauki Darasin Rayuwa Mai Yawa A Wajen Marigayi Galadiman Kano -Ahmad Rabi’u

Daga Ibrahim Muhammad

Babban Daraktan Gudanarwa na Tashar Tsandauri ta Dala, Alhaji Ahmad Rabi’u ya bayyana marigayi Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi da cewa mutum ne mai haƙuri, tawakkali da dattako.

Ya ce sun yi ailki da marigayin kusan shekaru 40 da suka wuce, yana shugaban mayankar Kano, shi kuma yana wakiltar Alhaji Aminu Ɗantata a matsayin darakta a mayankar.

Alhaji Rabi’u, wanda kuma kuma tsohon shugaban cibiyar ciniki, kuma tsohon Kwamishinan kasuwanci na jihar Kano ne, ya ƙara da cewa ya koyi abubuwa masu yawa da suka haɗa da haƙuri da jagoranci daga gare shi.

Ya tabbatar da cewa ya ɗauki darasi mai na rayuwa da suka haɗa da na haƙuri da tawakkali a kan komai.

Alhaji Ahmad Rabi’u wanda tsohon babban Akanta ne na Alhaji Aminu Ɗantata ya ce, zaman da su ka yi na aiki da Galadiman Kano, Abbas Sanusi ya ga yadda yake jagorantar zaman su na daraktoci in al’amura suka taso yana fuskantarsu ya ba su dama a matsayinsu na matasa a lokacin su faɗi ra’ayinsu a kan abin da suke ganin ya dace, kuma ya karɓa.

Alhaji Ahmad Rabi’u ya ce a lokacin marigayi Galadima ya haɓɓaka mayankar Kano a matsayinsa na jami’in hukumar Native Authority, kuma mutum ne da ya ba da gagarumar gudunmawa wajen cigaban masarautar Kano.

Ya yi kira ga iyalan Galadiman Kano marigayi Abbas Sanusi a kan yin haƙuri da riƙe zumunci da yi masa addu’a a koyaushe.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?