Gwarzo Ya Yi Ta’aziiyyar Galadiman Kano

Daga Ibrahim Muhammad

“Marigayi Galadiman Kano mutum ne mai haƙuri, juriya da iya danne ɓacin ransa.”

Tsohon mataimakin Gwamnan jihar Kano, tsohon ƙaramin ministan gidaje, Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo ne ya bayyana hakan a yayin ziyarar ta’aziiyya da ya kai ga shugaban jam’iyyar APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas na rasuwar mahaifinsu Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi.

ATM Gwarzo ya ce sun zo yin ta’aziya ne na rashin uba, kaka, Galadiman Kano wanda an yi babban rashi, domin sun yi aiki da shi shekaru 14 da suka wuce a lokacin da yake mataimakin Gwamna lokacin Malam Ibrahim Shekarau.

Ya jaddada cewa mutum ne mai haƙuri sosai da juriya a kan abubuwa da yawa. “Sau da yawa ko da wani abu ya ɓata wa Galadima rai, amma sai ya haƙura ya kau da kai,” in ji shi.

Abdullahi Tijjani Gwarzo ya yi kira ga iyalai da ‘yan’uwa da al’ummar Kano su yi haƙurin wannan rashin da ya shafi Kano da Arewa da ma ƙasa gaba ɗaya, su kuma ‘ya’yansa su cigaba da haɗin kai a tsakaninsu.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?