Gwarzo Ya Yi Ta’aziiyyar Galadiman Kano

Daga Ibrahim Muhammad

“Marigayi Galadiman Kano mutum ne mai haƙuri, juriya da iya danne ɓacin ransa.”

Tsohon mataimakin Gwamnan jihar Kano, tsohon ƙaramin ministan gidaje, Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo ne ya bayyana hakan a yayin ziyarar ta’aziiyya da ya kai ga shugaban jam’iyyar APC na jihar Kano, Abdullahi Abbas na rasuwar mahaifinsu Galadiman Kano, Alhaji Abbas Sanusi.

ATM Gwarzo ya ce sun zo yin ta’aziya ne na rashin uba, kaka, Galadiman Kano wanda an yi babban rashi, domin sun yi aiki da shi shekaru 14 da suka wuce a lokacin da yake mataimakin Gwamna lokacin Malam Ibrahim Shekarau.

Ya jaddada cewa mutum ne mai haƙuri sosai da juriya a kan abubuwa da yawa. “Sau da yawa ko da wani abu ya ɓata wa Galadima rai, amma sai ya haƙura ya kau da kai,” in ji shi.

Abdullahi Tijjani Gwarzo ya yi kira ga iyalai da ‘yan’uwa da al’ummar Kano su yi haƙurin wannan rashin da ya shafi Kano da Arewa da ma ƙasa gaba ɗaya, su kuma ‘ya’yansa su cigaba da haɗin kai a tsakaninsu.

  • Related Posts

    Rasuwar Audu Manaja Babban Rashi Ne Ga Arewa Da Nijeriya -Sulaiman Hussain

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano An bayyana rasuwar fitaccen ɗan kasuwa a harƙar man fetur, Alhaji Abdullahi Ahmad, wanda aka fi sani da Audu Manaja, a matsayin babban rashi ga Arewa…

    Asibitin Ƙashi Na Dala Ya Karrama Hon. Abba Kabir Bichi Kan Gudummawar Da Yake Bayarwa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Asibitin Ƙashi na Tarayya da ke Dala, Kano, ya ba wa ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi, Hon. Abba Kabir Bichi, lambar karramawa bisa gudunmawa…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Rasuwar Audu Manaja Babban Rashi Ne Ga Arewa Da Nijeriya -Sulaiman Hussain

    Rasuwar Audu Manaja Babban Rashi Ne Ga Arewa Da Nijeriya -Sulaiman Hussain

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai A ADC Reshen Kano Kan Zargin Hana Waɗanda Ba ’Yan Kwankwasiyya Ba Takara

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai A ADC Reshen Kano Kan Zargin Hana Waɗanda Ba ’Yan Kwankwasiyya Ba Takara

    Sanata Hanga Ɗan Gwagwarmayar Siyasa Ne Mai Neman Sauyi Da Ci Gaban Al’umma – Maikarfi Dala

    Sanata Hanga Ɗan Gwagwarmayar Siyasa Ne Mai Neman Sauyi Da Ci Gaban Al’umma – Maikarfi Dala

    Asibitin Ƙashi Na Dala Ya Karrama Hon. Abba Kabir Bichi Kan Gudummawar Da Yake Bayarwa

    Asibitin Ƙashi Na Dala Ya Karrama Hon. Abba Kabir Bichi Kan Gudummawar Da Yake Bayarwa

    Gidauniyar NNPCL Ta Miƙa Na’urar MRI Ta Zamani Ga Asibitin Ƙashi Na Dala

    Gidauniyar NNPCL Ta Miƙa Na’urar MRI Ta Zamani Ga Asibitin Ƙashi Na Dala

    LEON Projects Ta Sami Lambar Karramawa Kan Aikin Gina Ɗakin MRI A Asibitin Ƙashi Na Dala

    LEON Projects Ta Sami Lambar Karramawa Kan Aikin Gina Ɗakin MRI A Asibitin Ƙashi Na Dala