Kotu Ta Aike Da ‘Yan TikTok Gidan Gyaran Hali A Kano

Daga Ibrahim Muhammad

Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta jihar Kano ke yi domin kawo ƙarshen ayyukan rashin ɗa’a da ke yawaita a kafafen sada zumunta na zamani, ta samu nasarar kama wasu matasa guda huɗu masu amfani da manhajar TikTok da ake zargi da nuna rashin tarbiyya da kalamai marasa ma’ana inda aka gurfanar da su gaban kotu domin fuskantar hukunci.

Wannan na ƙunshe ne a cikin sanarwa da Abdullahi Sani Sulaiman, jami’in yaɗa labarai na Hukumar ya raba wa manema labarai.

Tun da farko a zaman kotun bayan mai gabatar da ƙara Batista Garzali Maigari Bichi ya karantowa waɗanda ake zargi, Hafsa Hamisu (Zoom-Zoom), Usman Majidaɗi (Majidaɗi) Sumayya Muhammad (Summy Beby) da Usman Ibrahim (Maikalar Kuɗi), tuhume-tuhumen da ake musu dukkanninsu nan take suka amsa.

Sai dai Mai Shari’a Halima Wali ta kotun Noman Sland, ta ɗage sauraran ƙarar daga 28/5/2025 zuwa 2/6/2025, tare da ba da umarnin a ajiye su a gidan gyaran hali har ranar da za a dawo domin yanke masu hukunci.

Ko a watanin da suka gabata, Hukumar Tace Finafinai da Ɗab’i ta Jahar Kano, ta aike da irin wadannan matasa gaban kotu domin ladabtar da su, inda kotun bayan samun su da laifi ta yanke musu hukuncin ɗaurin shekara ɗaya ko zaɓin biyan tara N100,000 da wanda za su karɓe su da bisa sharaɗin irin haka ba za ta ƙara faruwa ba.

Wannan dai wani yunƙuri ne da Hukumar Tace Finafinai ta jihar Kano ke yi domin kawo gyara, tare da daƙile irin rashin tarbiyyar da wasu matasa ke nunawa a kafafen sada zumunta a jihar Kano, wanda yin hakan ya ci karo da tsarin al’ada ta zamantakewa, tare da koyarwar addinin Musulunci.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe