Duk Abin Da Ya Taso Na Cigaban Al’umma Gwamnatin Abba Kabir Sai Ta Ji Ra’ayin Jama’a -Bombay

Daga Ibrahim Muhammad

Babu abin da za mu ce sai godiya ga gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin Abba Kabir Yusuf bisa kulawa da take da al’amuran al’ummarta, wanda duk abin da ya taso ba ta gudanar da shi kai tsaye sai ta yi tuntuɓa ta ji ra’ayin al’umma.

Jagoran Kwankwasiyya na mazabar Gama jigo a jam’iyyar NNPP a jihar Kano ne ya bayyana hakan.

Ya ce cikin kuɗure-kuɗure da ake buƙatar kawo gyara a ciki na tsarin mulkin ƙasa, wasu daga ‘yan majalisunmu a Gwamnatin Tarayyar sun shigar da buƙatun irin waɗannan abubuwa da ake don gyara, don haka jihar Kano tana kan gaba wajen gudanar da gyare-gyare da ake so a yi na kundin tsarin mulki.

Hon. Muhammad Adamu Bomboy ya ce suna goyon bayan gwamnatin Kano da al’ummarta kan neman ƙarin jiha da ƙananan hukumomi, kwamiti da gwamnati sun kalli wannan buƙata.

Kuma in aka duba ɓangaren tsaro ya shiga wani yanayi, don haka ake so a sahale kowace jiha ta yi domin za su kawo gudunmawa ga inganta tsaro.

Ya ƙara da cewa idan aka yi ƙarin ƙananan hukumomi da ƙirƙirar jiha daga cikin Kano zai taimaka wajen kusanto da gwamnati kusa da al’umma, in aka duba akwai adadin yanki da yawan mutane da ya kamata a ce sun zama ƙaramar hukuma, amma sai ka ga wani Kansila a wani yankin ya fi ma wata ƙaramar hukumar, amma in aka samu ƙarin ƙananan hukumomi za a matso da gwamnati kusa da al’umma.

Hon. Bomboy ya ce tun zuwan wannan gwamnati ta Abba Kabir Yusuf tana gudanar da duk wani abu da ya shafi al’umma babu zancen bambancin siyasa kan irin ayyuka da ake na raya ƙasa da kuma yadda ake sauraren koke-koke na al’umma, kuma ana gudanar da gwamnati a buɗe, babu bambanci na ra’ayin jam’iyya ta janyo kowa, kuma ayyukanta ido na gani hannu ya taɓa ƙafa ta taka.

  • Related Posts

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Karamci da Mutumtaƙa: Dubban Jama’a Sun Cika Garin Kwankwaso a Ɗaurin Auren ’Ya’yan Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

    Daga: Ibrahim Muhammad, Kano Garin Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano ya cika maƙil da dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma wajenta, yayin da…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe