Al’ummar Minjibir Sun Karrama Mai Shari’a Hauwa Lawan Umar

Daga Ibrahim Muhammad

Mai Shari’a ta babban kotun jihar Kano, Hauwa Lawan Umar Minjibir ta muna farin ciki da gode wa Allah bisa zaɓo su da ƙungiyar Minjibir Solidarity Forum ta yi ta karrama su wanda hakan ba dabara ko hikimar su ba ce ba horewa ce ta Ubangiji suna gode masa da wannan karanci da ƙungiyar da take haɗa zumunci da haɗa kan al’ummar Minjibir ta yi musu.

Ta bayyana hakan ne da take zantawa da manema labarai bayan karɓar shaidar karramawar da aka gudanar a Minjibir

Ta ce yadda aka ɗauke su abin misali aka yaba aka nuna domin ‘yan baya ma su yi koyi da shi suna kuma gode wa iyayensu da suka ba su tarbiyya da ilimi har suka sami wannan dama har ake yi musu wannan karramawar.

Ta ƙara da cewa wannan karramawar ya daɗa musu ƙwarin gwiwa da karsashi na yin riƙo da gaskiya da amana.

Da kuma adalci da yin komai bisa aiki da ilmi da bin ɗoron doka, musamman a matsayinta na masu yin hukunci duk abin da ya kama na adalci idan ya zo gabanta za su yi, suna kuma addu’ar Allah ya yi musu jagoranci a kai.

Mai Shari’ar ta babban kotun jihar Kano, Hauwa Lawan Umar Minjibir ta yi kira ga al’ummar Minjibir su dage da yin ilimi da riƙe addini da riƙo da amana da waɗannan abubuwa guda uku babu inda mutum ba zai je a matakin rayuwa ba da yardar Allah.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe