An Roƙi Kakakin Gwamnan Kano Sanusi Bature Ya Fito Takarar Sanata

Daga Ibrahim Muhammad

Tsohon ɗan takarar kansila a mazaɓar Dawanau, Honarabul Abdullahi Ado Mai Kaza, ya bayyana babban daraktan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a na gwamnatin Kano, Alhaji Sanusi Bature Dawakain Tofa, a matsayin jigo kuma jajirtacce a yankin Kano ta tsakiya da ma Jihar Kano.

A zantawarsa da manema labarai a Kano, Abdullahi Ado Mai Kaza, ya ce DG Sunusi Bature yayi koyi ne da halin Gwamna Kano Injiya Abba Kabir Yusuf na kishi da tallafawa al’ummar Kano.

“A harka ta ilimi, lafiya, tallafa wa ‘yan jam’iyya da ma duk abin da ya shafi ciyar da ɗan Adam gaba, a cikin shekara 13 da mu ke a tafiyar Kwankwasiyya ba mu da haziƙi jajirtacce irin mai girma Sanusi Bature”

“Ba a daɗe ba a Dawakin Tofa akwai marayun da ba su da yadda za su yi, Sunusi Bature da ya samu labari nan da nan ya saya masu gida ya ba su, haka kuma a satin da ya gabata ma mai girma DG ya tallafa wa makarantar Islamiyya da kuɗi fiye da miliyan ɗaya, ire-iren waɗannan abubuwan alherin ba sa ƙirguwa”, in ji Abdullahi Mai Kaza.

Daga nan ne ya yi kira da kakakin na gwamnan Kano Sunusi Bature da ya fito takararar Majalisar tarayya mai wakiltar Dawakin Tofa, Tofa da Rimin Gado, a cewarsa in ya so jaritaccen ɗan majalisa Hon. Injiniya Abdulƙadir Joɓe sai ya fito takarar Sanata a yankin namu mai albarka.

  • Related Posts

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Karamci da Mutumtaƙa: Dubban Jama’a Sun Cika Garin Kwankwaso a Ɗaurin Auren ’Ya’yan Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

    Daga: Ibrahim Muhammad, Kano Garin Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano ya cika maƙil da dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma wajenta, yayin da…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe