Ba Mu Da Wata Alakar Kasuwanci Da IPMAN – Matatar Dangote

...

Shugabannin matatar man Ɗangote sun yi watsi da rahotannin da ke cewa an ƙayyade farashin man fetur a kan naira 600 kan kowacce lita, inda ta bayyana rahotannin a matsayin jita-jita marar tushe.

A wata sanarwa da babban jami’in kula da harkokin kasuwanci da sadarwa na rukunin kamfanonin Dangote, Anthony Chiejina, ya fitar a shafin sada zumunta na X, ya yi tsokaci kan jita-jitar da ake ta yaɗawa da ke cewa matatar na tattaunawa da ƙungiyar dillalan man fetur ta ƙasar IPMAN, a kan yadda za a cimma matsaya wajen sayar da man a kan naira 600 kan kowacce lita.

Kamfanin ya fayyace cewa bai ƙulla wata yarjejeniya da ƙungiyar ta IPMAN ba, ya kuma jaddada cewa duk wani mataki da kamfaninsu ko matatar za ta ɗauka za a sanar a hukumance.

Sanarwar ta cewa “An jawo hankalinmu kan labarin da ke cewa kamfanin Dangote ya ƙayyade farashin man fetur kan naira 600 kan kowace lita, a jiya Talata, 13 ga watan Agustan 2024.”

“Za mu so mu fayyace cewa ba mu da wata alaƙar kasuwanci da IPMAN a yanzu.”

Ya ce “Ba mu taɓa tattaunawa kan farashin man fetur da IPMAN ba kuma ba su da wani hurumin yin magana a madadinmu

Related Posts

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Jihar Zamfara ta zama zakara a fannin kula Cibiyoyin kula da kiwon lafiya a matakin farko a duk faɗin yankin Arewa maso Yammacin ƙasar nan. Sunan Zamfara ya fito ne…

Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun