Ba Za A Haɗa Gwamnatin Abba Kabir Da Ta Ganduje Ba -Bello Sumaila

Daga Ibrahim Muhammad

Jigo a siyasar yankin Sumaila da ke kudancin jihar Kano, Hon. Bello Musa ya bayyana cewa yanayin ayyukan raya ƙasa da gwamnatin Abba Kabir Yusuf take masu kyau da inganci, ba za a kwatanta da gwamnatin APC ta Dakta Abdullahi Umar Ganduje ba.

A lokacin da yake zantawar da manema labarai a Kano, Hon. Bello Musa ya, “Har ga Allah muna ganin bambanci sosai a wannan gwamnatin idan aka kwatanta ta da ta baya. Ayyuka ga su nan ana ta yi i babu dare, ba rana a ko’ina ga hanyoyi ta ko’i’na,” ya tabbatar.

Alhaji Bello Musa Sumaila ya ce a yankinsu ƙaramar hukumar Sumaila ana yin hanyoyi da gyara makarantu, “In ka ga yadda aka gyara wata makarantar Firamare da ta shekara 90 ba za ka ce tsohuwa ba ce da kuma ayyuka na samar da ruwa da abubuwa da dama” ya bayyana.

Hon. Bello Musa Sumaila ya bayyana dalilinsa na shigowa Kano da cewa, “Mun zo ɗaurin aure ‘ya’yan mai bai Gwamnan rashawa kan siyasa, kuma taro ya yi taro, Allah ya ba da zaman lafiya, kuma ƙauna ce ta tara al’umma ba kuɗi aka bai wa kowa ba.

An bayyana mai bai wa Gwamnan jihar Kano shawara na musamman da cewa mutum ne na kowa mai faɗa da cikawa, shi ya sa ake ce masa Kotun Ƙoli saboda yana yanke hukunci a kan gaskiya, kuma haka yake, shi ya sa mutane ke ganin kamarsa.

Ya ce shi al’amarin aure zama ne na haƙuri da juna. “Hausawa na cewa, zo mu zauna ne, zo mu saɓa. Ba ma kamar wannan zamani da kowa kusan zuciyarsa a kusa take, amma duk in aka yi haƙuri sai a zauna lafiya,” in ji shi.

  • Related Posts

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Karamci da Mutumtaƙa: Dubban Jama’a Sun Cika Garin Kwankwaso a Ɗaurin Auren ’Ya’yan Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

    Daga: Ibrahim Muhammad, Kano Garin Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano ya cika maƙil da dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma wajenta, yayin da…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe