‘Galadiman Kano Ya Bar Giɓi Mai Wahalar Cikewa’

Daga Ibrahim Muhammad

Ɗan kasuwa kuma shugaban rukunin kamfanonin HAMIR, Alhaji Hamisu Rabi’u Jingau, ya nuna mutuƙar alhininsa bisa rasuwar Galadiman Kano babban ɗan majalisar masarautar Kano, Alhaji Abbas Sanusi da ya rasu ranar Talata.

Ya yi nuni da cewa an yi rashi na jagora da kullum yake ƙoƙarin haɗa kan al’umma da nusar da su muhimmancin zaman lafiya gare su.

Alhaji Hamisu Rabi’u, wanda ya bayyana hakan da yake zantawa da ‘yan jarida a yayin da ya kai ziyarar ta’aziyya gidan marigayin
ya ce, a matsayinsu na masu tasowa za su cigaba da koyi da halaye managarta na irin waɗannan magabata da suka bayar da gunmuwa wajen haɗin kan al’umma da mutuntawa.

Shi ma a yayin ta’aziyyar, shugaban kamfanin taki na ALYUMA, Alhaji Ali Maitaki ya ce, rashin Galadiman Kano Alhaji Abbas, rashi ne babba mai wahalar cikewa, musamman idan aka yi la’akari da irin gudunmuwa da suka bayar ga cigaban al’umma.

Alhaji Ali Maitaki ya ce, za a cigaba da tuna marigayi Galadima da irin gudunmuwa da ya bayar, su kuma al’umma da iyalansa za su yi haƙuri da wannan rashi da aka yi.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

    Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?