Gwamnan Zamfara Ya Biya Bashin Hakkin Ma’aikatan Jihar

Gwamnan jihar Zamfara Dauda Lawal ya kammala biyan bashin haƙƙin ma’aikatan da suka bar aiki na shekara da shekaru, tun daga shekarar 211, wanda ya kama Naira 9,357,743,281.35.

In dai za a iya tunawa, tun a watan Faburairun nan da ya gabata ne Gwamnan ya amince da a fara biyan basukan na Garatutin tsoffin ma’aikatan.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar yau a Gusau, ya bayyana cewa gwamnatin Zamfarar ta riga ta kammala biyan bashin Naira 4,860,613,699.22 rukuni-rukuni 9.

Haka kuma sanarwarta ce an biya tsaffin ma’aikatan Ƙananan Hukumomin jihar bashin su na Naira 4,497,129,582.13

Idris ya ce: A jajircewarsa na ganin ya inganta aikin gwamnatin jihar Zamfara, a watan Faburairu Gwamna Lawal ya ƙaddamar da wani kwamitin da zai tantance duk ilahirin tsaffin ma’aikatan jihar da ba a biya su haƙƙoƙin su ba, tun daga shekarar 2011.

“Ya zuwa yanzu, cikin mutum 3,880 da aka tantance, mutum 2,666 sun karɓi haƙƙoƙin su, wanda ya kai ma Naira 4,860,613,699.22, daga cikin basukan da aka biyo gwamnatocin baya. An biya waɗanda suka bar aiki daga shekarar 2015 zuwa 2024.

“A ɗaya ɓangaren kuma, mutum 3,840 cikin ma’aikatan Ƙananan Hukumomi da Malaman Firamare 4,804 da aka tantance sun karɓi haƙƙoƙin su a rukunai 9, wanda ya kai ma kuɗi Naira 4,497,129,582.13. Haƙƙoƙin barin aiki na Garatuti da Ƙananan Hukumomi ke bi ya kai ma Naira 5,688,230,607.20, wanda yanzu haka an biya Naira 4,497,129,582.13. Waɗanda suka bar aiki a tsakanin shekarun 2011- 2021 ne suka amfana.

“A taƙaice dai, ya zuwa yanzu gwamnatin jihar ta biya Tsoffin ma’aikatan jiha da na Ƙananan Hukumomi da ya kai ma Naira 9,357,743,281.35 daga baussukan Naira 13,784,179,513.80 da tsaffin ma’aikatan suka biyo, wato Mutum 6,506, cikin mutum 8,684 da aka tantance. Su ne kuma waɗanda suka bar aiki a tsaknin shekarun 2011- 2024.”

Related Posts

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

Daga Ibrahim Muhammad An yi kira ga mata da su ƙara jajircewa wajen karatun fannin zayyana gine-gine (Architecture) domin bayar da gudunmawa ga bunƙasa cigaban al’umma. Wannan kira ya fito…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History