Gwamnan Zamfara Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Garin Mada

  • Ya sha alwashin hukunta waɗanda suka kashe Malamin

A yau Juma’a ne Gwamnan Jihar Zamfara Dauda Lawal ya ziyarci garin Mada domin yin ta’aziyyar rasuwar babban Limamin garin, Marigayi Sheikh Abubakar Mada.

Idan za a iya tunawa, wasu da ake zargin ’yan banga ne suka kashe Sheikh Abubakar Hassan Mada a makon jiya a garin Mada da ke Ƙaramar Hukumar Gusau ta Jihar Zamfara.

A wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa Gwamna Lawal ya yi sallar Juma’a ne a masallacin garin Mada.

A cewar sanarwar, Gwamnan ya miƙa ta’aziyya ga iyalan marigayi Sheikh Abubakar Hassan Mada, Hakimin gundumar, da sauran al’ummar yankin.

A yayin jawabinsa ga jama’a bayan sallar Juma’a, Gwamna Lawal ya yi alƙqwarin yin duk mai yiwuwa don ganin an yi adalci a kan lamarin.

“Na zo nan ne domin in tabbatar wa mutanen garin Mada cewa gwamnatina ta himmatu wajen ganin an tabbatar da adalci, tare da hukunta waɗanda suka aikata wannan aika-aika.

“Babu wani abu da za a bari wajen ganin an tabbatar da adalci a kan kisan Sheikh Abubakar. Za mu yi aiki tuƙuru don ganin cewa marigayi Sheikh da iyalansa sun samu adalcin da ya kamata,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta nakalto gwamnan yana cewa, “Bana Gusau lokacin da lamarin ya faru, amma bayan na samu wannan labari mai tada hankali, nan take na tuntuɓi shugabannin hukumomin tsaro da abin ya shafa a jihar domin ɗaukar matakin da ya dace”.

“’Yan sanda sun fara gudanar da bincike cikin gaggawa kan kisan gillar. Na rantse da Allah za mu tabbatar da cewa duk wanda aka samu da laifi a wannan ɗanyen aikin, za a hukunta shi,” in ji sanarwar.

Related Posts

Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

Karamci da Mutumtaƙa: Dubban Jama’a Sun Cika Garin Kwankwaso a Ɗaurin Auren ’Ya’yan Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

Daga: Ibrahim Muhammad, Kano Garin Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano ya cika maƙil da dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma wajenta, yayin da…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Breaking the Chains of Godfatherism: Uba and Fubara’s Path to Autonomous Politics

Breaking the Chains of Godfatherism: Uba and Fubara’s Path to Autonomous Politics

Maryam Abacha Accepts Posthumous Doctorate for Late Gen. Abacha, Describes Honour as Well-Deserved

Maryam Abacha Accepts Posthumous Doctorate for Late Gen. Abacha, Describes Honour as Well-Deserved

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara