Gwamnati Na Shirin Ɓullo Da Hanyar Sauƙaƙa Harkar Sufuri Ga Al’ummar Kano -Shugaban KAROTA

Daga Ibrahim Muhammad

Gwamnatin jihar Kano na kan gaba wajen abin da ya shafi kyautata jin daɗin ma’aikata a ƙasar nan, shi ya sa ma’aikata suka fito suke nuna gamsuwa da tagomashi da ayyukan alkhairi da Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf yake tanadar musu a wannan taro na bukin ranar ma’aikata.

Manajan daraktan Hukumar KAROTA na jihar Kano, Injiniya Faisal Muhammad ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida a taron ranar ma’aikata ta duniya a Kano.

Ya ja hankalin ma’aikatan jihar Kano a kan yin riƙo da gaskiya da yin adalci a duk wani aiki da suke. “Su mai da hankali a kan haƙƙi da sauke nauyi da Allah ya ɗora musu,” in ji shi.

Faisal ya ce dukkan wani ma’aikaci akwai alƙawari tsakaninsa da Ubangiji da al’ummarsa, saboda haka a tsaya a kiyaye wannan alƙawari domin jihar Kano ta cigaba a yi nasara a kan abin da aka sa a gaba.

Ya ce akwai shiri da mai girma Gwamna yake da shi na ɓullo da tsari na sauƙaƙa harkar sufuri ga al’ummar jihar Kano kamar yadda aka samar ake sauƙaƙawa ɗalibai ta hanyar samar musu motoci.

Shugaban na Hukumar KAROTA, ya ce sauran al’umma ma akwai shirin da Gwamnan jihar Kano da Kwamishinan Sufuri suka yi masu a kan yadda za a samar da motoci da za su sauƙaƙa zirga-zirga cikin rahusa ba tare da al’umma sun jigata ba, ganin irin halin da al’umma ke ciki na matsin rayuwa.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe