Gwamnatin Kano Ta Kama Na’urorin Da Ake Bugu Wa Masu Tallan Maganin Gargajiya Hotunan Batsa

Daga Ibrahim Muhammad

A wani salo na tabbatar da doka tare da kawo tsafta a ɓangaren ɗab’i, Hukumar tace finafinai da Dab’i ta Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Alhaji Abba El-mustapha ta yi nasarar ganowa tare da kama wasu na’urori da ake amfani da su wajen buga hotunan batsa ga masu sana’ar maganin gargajiya a wasu unguwannin Jihar Kano.

Wannan na cikin wata sanarwa da Abdullahi Sani Sulaiman Jami’in yaɗa labarai na Hukumar ya raba wa manema labarai.

Kayayyakin da aka kama sun haɗa da kwamfutoci da kuma injunan buga hotuna.

Da yake holin kayan da Hukumar ta kama, Alhaji Abubakar Zakari Garun Babba Darakan Dab’i na hukumar ya bayyana wuraren da aka kama waɗannan kayayyakin da suka haɗa da wasu unguwanni a ƙaramar Hukumar Birni da wasu ƙauyuka a ƙaramar Hukumar Wudil.

Garun Babba ya nuna taikacinsa kan yadda wasu ke fakewa da sana’ar buga takardu suke buga hotunan batsa.

Ya yi gargaɗin cewa Hukumar ba za ta lamunci hakan ya cigaba da faruwa a faɗin Jihar Kano ba.

Hukumar na cigaba da riƙe kayan inda take dakon shawarar lauyoyinta domin ɗaukar mataki na gaba.

Garun Babba ya gargaɗi masu sana’ar buga takardu da su shiga taitayinsu domin gujewa fushin doka. Ya yi kira ga al’umma da jami’an tsaro a kan su cigaba da bai wa Hukumar cikakken goyan baya da haɗin kai, domin samun nasarar kawo ƙarshen irin waɗannan ayyukan a faɗin jihar Kano.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe