Gwamnatin Zamfara Tana Na Jiran Shawara Ma’aikatar Shari’a Biyan Tsafin Mataimakan Shugabanin Kananan Hukumomi Da Kamsilolisu

Daga Hussaini Yero

Kwamishinan Kananan hukumomi na jihar Zamfara, Injiniya Ahmed Garba Yandi ya ce suna jiran shawarar kwararru kan batun biyan alawus na sama da Naira biliyan 5 da kungiyar tsofaffin mataimakan shugabanin Kananan hukumomi da Kansiloli na Jamiyyar APC da ta sha kayi suka nemi gwamna Dauda Lawal na Jamiyyar PDP.da ya biyasu hakokin su.

Da yake amsa tanbayoyin manaima labarai a ofishin sa kan batun, Kwamishinan ya amince da karbar takardar bukatun nasu wanda daga bisani aka mika wa ma’aikatar shari’a ta jihar domin samun shawarwari akan koken nasu.

Injiniya Yandi, ya bayyana cewa, ma’aikatarsa ba za ta iya daukar wani mataki kan lamarin ba saboda la’akarin da doka ta shafa wanda dole ne a yi karin haske akanta.

Sai dai a nasa ra’ayin Injiniya Ahmed Garba Yandi ya yi mamakin da ya sa basu nemi a biya su alawus-alawus daga gwamnatin da baya da suka yi aiki da itaba,dan suna da isashen lokacin na biyan su kakokin su tunda sune sukayi ma aiki.a mukamin Siyasa .Amma da ace ma’aikata ne wannan muna da haki mu biyasu ,kuma yanzu haka munbiyasu hakokin su ,su ma’aikatan da gwamnatin baya ta gaza biyan su nasu hakokin,na Albashi, alawus da na wadanda suka aje aiki.

Kwamishinan ya jaddada cewa, ma’aikatar za ta yi hakuri ta dauki matakin da ma’aikatar shari’a za ta bayar kan batun kafin daukar mataki na gaba.

Idan dai za a iya tunawa kungiyar tsofaffin Shugabannin Kananan hukumomi da kansilolin jihar Zamfara,karkashin mulkin tsohon gwamna Mtawale sun bukaci tare da yin kira ga gwamnatin jihar da ta biya wa mambobinta sama da Naira biliyan 5 na alawus-alawus din sallamar wadanda ta ce suna matukar bukatar tallafin kudi domin kula da iyalansu.

Related Posts

Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

Karamci da Mutumtaƙa: Dubban Jama’a Sun Cika Garin Kwankwaso a Ɗaurin Auren ’Ya’yan Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

Daga: Ibrahim Muhammad, Kano Garin Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano ya cika maƙil da dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma wajenta, yayin da…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

Convoluted and Confused Political Situation and Insecurity: A Stop-Gap to State Collapse in History

Breaking the Chains of Godfatherism: Uba and Fubara’s Path to Autonomous Politics

Breaking the Chains of Godfatherism: Uba and Fubara’s Path to Autonomous Politics

Maryam Abacha Accepts Posthumous Doctorate for Late Gen. Abacha, Describes Honour as Well-Deserved

Maryam Abacha Accepts Posthumous Doctorate for Late Gen. Abacha, Describes Honour as Well-Deserved

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko

Zamfara Ce Ta Ɗaya A Yankin Arewa Maso Yamma A Fannin Cibiyoyin Kula Da Lafiya A Matakin Farko