Karrama Kwankwaso: An Ajiye Ƙwarya A Gurbinta Ne -Hon Nura Dala

Daga Ibrahim Muhammad

Babban hadimi na musamman ga Sanatan Kano ta Tsakiya, Hon. Nura Mai Ƙarfi Dala, ya bayyana karramawar da Jami’ar Kimiyya da Fasaha ta Aliko Ɗangote da ke Wudil, Kano ta yi wa Jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da digirin girmamawa da cewa an ajiye ƙwarya a gurbinta ne.

Ya ce ba Kwankwaso digirin girmamawar tabbas an yi abin da ya kamata, musamman idan aka yi la’akari da irin gudummuwa da ya bai wa jihar kano a ɓangaren ilimi.

Hon. Nura Me Ƙarfi Dala, ya yi nuni da cewa su ma waɗanda Jami’ar ta karrama da suka haɗa da shugaban kamfanin AMASCO, Alhaji Mustapha Ado da Alhaji Ɗahiru Barau Mangal da Alhaji Aliko Ɗangote a matsayin iyayen Jami’ar, mutane ne da Allah ya horewa arziƙi suke yin hidima ga al’umma. Ya roƙi Allah ya yawaita irin su, sannan kuma ‘yan baya da suke tasowa su yi koyi da su wajen ba da gudunmuwa ga cigaban al’umma.

Ita ma Hajiya Rahana Iliyasu mai bai wa shugaban ƙaramar hukumar Kumbotso a Kano shawara kan harkokin mata ta ce, duk ɗaukakar da Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso ke samu daga Allah ne, saboda irin kishinsa da son cigaban a’umma, musamman talakawa. “Don haka yake ta samun ɗaukaka a rayuwarsa”, in ji ta.

Da yake zantawa da manema labara, Alhaji Shehu Tijjani mai kula da ofishin Sanatan Kano ta Tsakiya, Rufa’i Sani Hanga ya ce, waɗanda aka karrama tun daga Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, Aliko Ɗangote, Alhaji Mustapha AMMASCO da Alhaji Ɗahiru Barau Mangal, suna ba da mutuƙar gudunmuwa wajen tallafawa cigaban ilimi.

  • Related Posts

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Karamci da Mutumtaƙa: Dubban Jama’a Sun Cika Garin Kwankwaso a Ɗaurin Auren ’Ya’yan Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

    Daga: Ibrahim Muhammad, Kano Garin Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano ya cika maƙil da dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma wajenta, yayin da…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe