KUNGIYAR KAFIGAN TA YI JIMAMIN RASUWAR GALADIMAN KANO.

Da cikakken alhini da juyayi, kungiyar ‘Kannywood Film Industry Guilds and Associations (KAFIGAN)’ na mika ta’aziyyarta ga al’ummar Jihar Kano baki daya, bisa rasuwar Alhaji Abbas Muhammadu Sanusi, Galadiman Kano kuma babban jigo a masarautar Kano.

Marigayi Galadiman Kano, wanda ya rasu yana da shekaru 92 bayan jinya mai tsawo, ya bar ‘ya’ya da jikoki da dama. Daga cikin ‘ya’yansa akwai Alhaji Abdullahi Abbas, shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jJihar Kano.

Shugaban kwamitin Amintattu na KAFIGAN, Alhaji Isma’il Na’Abba (Afakallah), ya bayyana marigayin a matsayin ginshiki mai mahimmanci a tsarin masarautun gargajiya, wanda gudunmawarsa wajen ci gaban masarautu da adana al’adu za su kasance abin tunawa ba ma a Jihar Kano kadai ba, a kasar da ma duniya baki daya.

Isma’il Na’Abba Afakallah ya mika ta’aziyya ga gwamnatin Jihar Kano, majalisar masarautar Kano, da iyalan marigayin, tare da yin addu’a Allah Ya gafarta ma sa kuma Ya sa Jannatul Firdausi makoma a gare shi.

Sa hannu:
Al-Amin Ciroma
Daraktan Yada Labarai da Harkokin Jama’a.

Related Posts

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?