Kyakkyawan Mua’malar Hon. Sanusi Surajo Ta Sa Ɗimbin Al’umma Ke Taruwa A Sha’aninsu -Amb. Yahaya Talba

Daga Ibrahim Muhammad

An bayyana ɗimbin jama’a da suka zo ɗaurin auren na gidan mai bai wa Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf shawara na musamman a kan harkokin siyasa, Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso da cewa ya nuna irin kyakkyawar mu’amala da tsari da yake ga dukkan al’umma, shi ya sa mutane suke tare da shi a dukkan sha’aninsu.

Mataimakin shugaban jam’iyyar NNPP na jihar Kano, Ambasada Hon. Isyaku Yahaya Talba ne ya bayyana hakan da yake zantawa da ‘yan jarida a garin Kwankwaso.

Ya yi fatan Ango da Amarya Allah ya zaunar da su lafiya da yin haƙuri da juna, Allah ya sa albarka a auren, ya kawo alheri da zuriyya nagari ɗayyaba.

Ya ƙara da cewa yadda al’umma ta taru don shaida auren ya nuna duk jihar Kano ba wata jam’iyya bayan ta NNPP, kuma babu wani Jagora da ya wuce Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso.

Sun gode wa Allah da ya zama tsarin Kwankwasiyya yana haifa da alkhairi mai yawa a tsakanin jama’a.

Talba ya ƙara da cewa irin ayyuka da mai girma Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf yake na kulawa da cigaban al’umma birni da karkara, mutane suna gamsuwa da tsarin gwamnatinsa da tsarin Kwankwasiyya.

Ambassada Isyaku Yahaya Talba ya ce, suna fata a zaɓen 2027 Jagoran Kwankwasiyya Dakta Rabi’u Musa Kwankwaso ya zama shugaban ƙasar Nijeriya gaba ɗaya domin zai kai ta ga tudun-mun-tsira.

  • Related Posts

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya damƙa Lambar Karramawa ta Ƙasa a Ayyukan Hidimta wa Al’umma (NEAPS) 2025 ga Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, bisa ayyukan da gwamnati ta gudanar…

    Tsarin Kwankwasiyya Ne Ya Fi Dacewar Da Al’ummar Kano -Injiniya Iliyasu Usman

    Daga Ibrahim Muhammad An bayyana ƙaramar hukumar Nasarawa da ke jihar Kano da cewa suna zaune lafiya babu rigimar siyasa ko wani abu na daban a tsakanin ‘yan Kwankwasiyya, jagorancinsu…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe