MAULIDI: Gwamna Dauda Lawal Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

MAULIDI: Gwamna Dauda Lawal Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya buƙaci a ƙara addu’o’in samun zaman lafiya a jihar da ma Nijeriya baki ɗaya.

Gwamnan ya yi wannan kira ne a ranar Juma’a domin murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris ya fitar a Gusau, ya bayyana cewa Musulmi na gudanar da bukukuwan Mauludin Annabi duk shekara a ranar 12 ga watan Rabiul Awal, wata na uku na Hijira.

“Gwamna Dauda Lawal a madadin al’ummar jihar Zamfara yana taya al’ummar Musulmi murnar zagayowar ranar haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW).

“Kowace ranar 12 ga watan Rabi’ul Auwal rana ce ta murnar zagayowar ranar haihuwar Manzonmu mai albarka (SAW).

“Wannan lokaci ne mai kyau da ya kamata dukkan Musulmi su yi koyi da rayuwar Manzon Allah (SAW).

“Musulunci ba addini kawai ba ne, hanya ce ta rayuwa, rayuwar Annabi (SAW), ta shiryar da mu zuwa ga kyawawan ɗabi’u, halaye da ayyuka.

“Ya kamata mu yi amfani da irin waɗannan muhimman lokuta na addini domin mu dage da addu’o’in samun zaman lafiya a Jihar Zamfara, Arewa maso Yamma, da ƙasa baki ɗaya.

“Allah (T) ya kawo mana ƙarshen ta’addanci da duk wani nau’in aikata laifuka a cikin al’ummarmu.”

Related Posts

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?