Ministan Sufuri Ya Yaba Wa Izala Kan Shirya Musabakar Ƙur’ani

Daga Ibrahim Muhammad, Kano

Ministan Sufuri, Sanata Ahmed Alƙali ya yaba wa ƙungiyar Izala ta ƙasa ƙarƙashin jagorancin Sheikh Sani Yahaya Jingir bisa jajircewa wajen shirya aikin alkhari na ilimi da ilmantar wa musamman a kan abin da ya fi komai muhimmanci a harkar ilimi wato ilimi a kan Ƙur’ani.

Ministan ya yi wannan bayani ne ta bakin babban mataimakansa Farfesa Shu’aibu Abdullahi Ɗan’wanka a wajen rufe musabaƙar Ƙur’ani da ƙungiyar ta gudanar a Kano na tsawon mako daya.

Ya ƙara da yi wa ƙungiyar da shugabannin ta da masu hidimta ta mata fatan alkhari. Ya jinjina musu da yaba wa ƙwazon dukkan ‘yan takara da suka shiga musabaƙar da suka fito daga jihohin ƙasar nan har ma da na jamhuriyar Nijar da Ghana.

Ministan ya ƙara da cewa a shirye yake ya ci gaba da ba da gudunmuwa a duk wani abu da ya taso a ƙungiyar domin bunƙasa koyarwar addinin Musulunci.

Ministan Sufurin ya gode wa ƙungiyar ta Izala bisa ƙaranci da girmamawa da aka yi masa na gayyatarsa taro na alkhairi na musabaƙar Ƙur’ani na ƙasa kashi na 28 a jihar Kano wanda hakan babban karamci ne a gare shi .

Farfesa Shu’aibu Abdallah Ɗan’wanka ya ba da haƙuri a madadin Ministan na Sufuri kasancewar ba shi ne ya zo da kansa ba sai wakilci saboda wasu dalilai na aiki da suka taso masa.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe