Mun Ji Daɗin Naɗe-Naɗen Sarautan Da Sarkin Kano Sanusi Ya Yi -Hajiya Hadiza Sardaunan Mata

Daga Ibrahim Muhammad

Hajiya Hadiza Ali Bala, ɗaya daga cikin ‘ya’yan marigayi Galadiman Kano Abbas Sanusi da aka fi sani da Hajiyar Masallaci, kuma ake kiran ta da Sardaunan Mata ta bayyana naɗin da Sarkin Kano Muhammad Sanusi ya yi wa Yariman Kano daga gidansu abin farin ciki ne gare su zuriyar marigayi Galadiman Kano, Abbas Sanusi.

Ta bayyana hakan ne a yayin wata liyafar da aka shirya ta taya murna ga wasu daga waɗanda aka yi wa sabbin naɗe-naɗen mayan sarautu a fadar Kano.

Ta ce ta yi mutuƙar jin daɗin yadda ta ga al’umma suka zo daga sassa daban-daban daga ciki da wajen jihar Kano suka taya su murnan wannan naɗin da Sarkin ya yi a masarautar Kano.

Ta ce wannan naɗe-naɗen mukamai da aka yi duk sun shafe ta domin wanda aka bai wa Galadima a yanzu Baba Mannir Uba ne a gare ta. Hhaka wanda aka bai wa Wambai ɗan’uwnata ne, kuma ƙaninta. Haka shi ma wanda aka bai wa Yariman Kano Ahmad Abbas Sanusi, wanda suke kiran sa Ɗan Darman ƙaninta ne, kuma ɗanta.

Hajiya Hadiza Ali Bala Sardaunan Mata ta yi fatan dukkan waɗanda aka naɗa a muƙaman a masarautar Kano, Allah ya ba su ikon riƙewa da sauke nauyin da aka ɗora musu.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe