NDLEA Ta Kama Waɗanda Suka Raunata Jami’inta A Kano

Daga Ibrahim Muhammad Kano

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa (NDLEA) reshen jihar Kano, ta kama matashin da ya soki jami’inta da makami a yunƙurinsu na tserewa da kayan mayen da suke ɗauke da shi.

Sadiq Muhammad Maigatari ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya aika wa manema labarai a safiyar Laraba ya ce, lamarin ya faru ne a shatele-talen Rahama da ke ƙaramar hukumar Bebeji a jihar Kano.

Ya ce sun kama natasan Musa Usman da Buhari Ya’u Bashir, a lokacin da suke ƙoƙarin shigowa da kayan mayen samfurin Tabar Wiwi Kilogram 1.1, Diazepam grams 8 (Fakiti 38), da kuma Exol grams 59 (Fakiti 165)”.

Ya ƙara da cewa, “A yayin da jami’anmu na Shiyyar Ƙiru suke ƙoƙarin kama su ne shi Musa Usman, ya ji wa jami’inmu mummunan rauni ta hanyar sukar sa da Ɗanbuda.”

Kwamandan hukumar na jihar Kano, Abubakar Idris Ahmad ya yi Allah-wadai da wannan ɗanyen aiki da suka yi, har ma ya ba da tabbacin irin wannan ɗabi’a ta masu aikata laifin ba za ta sare musu gwiwa ba.

Sadiq Mai Gatari ya ce yanzu haka suna gudanar da bincike a kan waɗanda ake zargin, kuma za su gurfanar da su a gaban kotu bisa zargin su da aikata laifukan safarar kayan maye da kuma cin zarafin jami’in hukumar.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe