Sallah: Turmutsitsi A Filin Idin Gombe Ya Hallaka Ƙananan Yara 2, Wasu 20 Sun Jikkata

Daga Khalid Idris Doya

A wani ibtila’in da ya faru a ranar Idi a jihar Gombe, wasu ƙananan yara biyu (mata) sun rasa rayukansu a babban filin Idin Gombe biyo bayan faruwar wani turmutsitsi.

Wakilinmu ya labarto cewa lamarin ya faru ne wajajen ƙarfe 10:45 na safiya jim-kaɗan bayan kammala sallar nafila mai raka’a biyu ta karamar Sallar 2025 wanda babban limamin Gombe ya jagoranta kuma gwamna Muhammad Inuwa Yahaya da Sarkin Gombe, Abubakar Shehu Abubakar suka halarta.

Ɗan rahotonmu ya labarto cewa turmutsitsin ya faru ne a kofar fita yayin da jama’a suke ta ƙoƙarin fita daga filin Idin.

An kuma tattaro cewa wasu ƙarin masallata su 20 sun jikkata bayan biyu da suka rasu.

Rundunar ‘yansandan jihar Gombe ta bakin kakakinta Buhari Abdullahi, ta tabbatar da faruwar lamarin.

A cewarsa, akwai ɗimbin jama’a da suka haɗa da mata da ƙananan yara da suka yi ta ƙoƙarin gaggawar ficewa daga filin Idin, wanda tare da tsananin zafin da ake yi, hakan ya kai ga haifar da turmutsitsin.

“A sakamakon hakan, mutum 22 ne lamarin turmutsitsin ya shafa.

“Cikin gaggawa motar ɗaukar marasa lafiya daga gidan gwamnati ta kwashi waɗanda suka raunatan zuwa asibitin Zainab Bulkachuwa, yayin da sauran bakwai kuma aka kaisu zuwa asibitin koyarwa ta gwamnatin tarayya da ke Gombe domin nema musu kulawar likitoci.

“Abun takaici, mutum biyu daga cikin waɗanda lamarin ya shafa likita ya tabbatar da mutuwarsu a lokacin da suke karɓar magani, su ne masu suna: Aisha Salisu Ahmed, ‘yar shekara hudu da rabi a duniya da kuma Maryam Abdullahi Gwani, ita ma ‘yar shekara 4,” ya shaida.

Rundunar ta bai wa masu kula da filin Idin shawara da cewa a nan gaba suke tabbatar da sun bude dukkanin ƙofofin wurin domin kauce wa sake faruwar irin wannan lamarin a nan gaba.

Related Posts

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jaruman Masana’antar Kannywood, ƙarƙashin ƙungiyarsu ta ƙasa, sun kai ziyarar girmamawa ga tsohon Kwamishinan Sufuri na Jihar Kano, Ibrahim Ali Namadi Dala. A yayin ziyarar, ƙungiyar…

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya jagoranci zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar karo na 58 tun bayan hawansa mulki a shekarar 2023, abin da gwamnatin jihar ta ce ya zama…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Ƙungiyar Jaruman Kannywood Sun Kai Wa Hon. Ibrahim Ali Namadi Dala Ziyarar Girmamawa

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Jagoranci Zaman Majalisar Zartarwa Ta 58 A Zamfara

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

Mata Su Dage Wajen Karatun Fannin Zayyana Gine-Gine (Architecture) -Arc. Binta Ahmad Umar

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

An Buɗe Sabon Masallacin ’Yan Nama a Kasuwar Sabon Gari, Kano

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Why I Cannot Approach the Court on the Bekwarra LGA Matter?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?

Waɗanne Nasarorin Hukumar Taimakekeniyar Kula da Lafiya ta Jihar Kano Ta Cimma?