Sarkin Kano Ya Naɗa Abdullahi Sarki Muhammad Sarkin Yamma

Daga Ibrahim Muhammad Kano

Sarkin Yamman Kano Alhaji Abdullahi Sarki Muhammad ya bayyana godiya bisa dama da Allah ya ba shi aka zaɓe shi a cikin mutane da yawa ba domin ya fi wani ba Sarkin Kano Malam Muhammad Sanusi ya ga ya cancanta ya naɗa shi a sarautar Sarkin Yamma.

Ya bayyana haka ne da yake zantawa da manema labarai a gidansa jim kaɗan bayan naɗin da aka yi masa.

Alhaji Abdullahi Sarki Muhammad ya ƙara da godiya ga Allah bisa wannan sabuwar sarauta da aka ba shi wacce ba a taɓa yin ta a Kano ba, ita ce ta farko da Allah ya nufa shi aka soma yi wa a wannan lokaci.

Sabon Sarkin Yamman na masarautar Kano Alhaji Abdullahi Sarki Muhammad ya ce kasancewar sarautar baƙuwa ce a Kano suna shirye da yin biyayya da yin ayukka da Maimartaba Sarkin Kano Malam Muhammad Sanusi zai ɗora musu nauyin gudanarwa a masarautar.

Ya ce muhimmin abin da za su yi shi ne su taimaka wajen ba da shawara wajen yadda za a tafi da mulki a ƙasar Kano yanzu abin da za su yi ke nan. “Ina matuƙar farin ciki da ni na soma rabauta da sarautar Sarkin Yamma. Ina godiya ga Allah bisa dama da ya ba ni,” in ji shi.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe