Sheikh Shariff Saleh Ne Zai Jagoranci Jana’izar Sheikh Ɗahiru Usman A Filin Idin Bauchi

Dubban ɗaruruwan al’ummar Musulmai za su hallara a yau Juma’a da misalin karfe 3 na rana (3pm) a babban filin Idin Bauchi domin gudanar da sallar jana’izar fitaccen Malamin addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi wanda ya rasu a ranar Alhamis.

Za a gudanar da jana’izar ne a babban filin Idi da ke Bauchi.

Babban aminin marigayin, Shariff Ibrahim Saley Al’husainiy, shi ne zai jagoranci sallar jana’izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi kamar yadda Marigayin ya bar wasiyyar hakan. Ana sa ran jama’a daga sassa daban-daban na Afrika ne za su halarci wannan jana’izar.

A sanarwar da ya fito daga gidan marigayi Sheikh Dahiru Usman, wanda M Daha Azhary Bauchi ya fitar ya shaida cewar, “Jana’izar Maulana Sheikh Dahiru Usman Bauchi….. Babban Amininsa Shariff Ibrahim Saley Al’husainiy, shi ne zai Jagoranci yi masa Sallah kamar yadda yyi Wasiyya.

“Za a yi Sallar ne a ranar Juma’a 28-11-2025 a babban filin Idi da ke Bauchi da ƙarfe 3:00 wato bayan Sallar Juma’a,” in ji M Daha Azhary Bauchi.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe