Shugaban APC Ya Nemi Afuwar Al’ummar Fagge, Kano Bayan Sun Maka Shi A Kotu

Daga Ibrahim Muhammad

Shugaban jam’iyyar APC na jihar Kano Kano Abdullahi Abbas ya nemi gafarar al’ummar Fagge game da maganganu da ake zargin na ɓatanci ne ga al’ummar abin da ya jawo fushi tare da shigar da shi ƙara a kotun Majistare da ke Kano.

An jiwo sautin neman gafarar ne da Abdullahi Abba ya yi a cikin wani sauti da Lauyan al’ummar Fagge, Barrister Abba Hikima Fagge, ya wallafa a shafinsa na Facebook, inda yake nuna cewa kuskuren fahimta aka yi masa a kan abin da ya faɗa. Ya ce shi ba shi da wata hujja ta wulaƙanta mutanen Fagge.

A kwanakin baya ne dai wasu mutum 10 cikin fitattun mazauna Fagge suka shigar da ƙara na zargin shugaban APC Abdullahi Abbas da yin kalaman ɓata suna da zai iya jawo tunzuri.

Masu shigar da ƙarar sun haɗa da Dakta Nuruddeen Abubakar, Sheikh Abubakar Ya’u, Alhaji Sani Salisu da sauran mutane bakwai a madadin su da sauran mutanen unguwar da ke son zaman lafiya.

Masu ƙarar sun buƙaci kotu ta ba da umarnin a gayyaci Abdullahi Abbas ya bayyana a gaban kotu. Lauyoyin da suka shigar da ƙarar sun nemi kotu ta yi amfani da tanade-tanaden dokar ACJL 2019 domin umartar Kwamishinan ‘yan sanda na Kano ya binciki Abdullahi Abbas kan zarge-zargen da suka shafi cin mutunc da ɓata suna da neman haddasa ƙiyayya tsakanin wasu jama’a.

An ce maganganun Abdullahi Abbas sun fito ne yayin gudanar da wani taron siyasa, inda aka ji yana danganta “duk wani mara ƙima” da Fagge, tare da wasu ƙarin kalamai da mazauna yankin suka ce suna iya haddasa rarrabuwar kai.

Sai dai Abbas ya dage cewa an fassara kalamansa ba daidai ba, kuma bai yi nufin wulaƙanta wani ba.

Kotun Majistare na shirin yanke hukunci kan buƙatun da aka gabatar a cikin kwanaki kaɗan masu zuwa, idan kuma an amince da haƙurin da ya bayar, hakan na nufin za a iya janye ƙarar.

  • Related Posts

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Karamci da Mutumtaƙa: Dubban Jama’a Sun Cika Garin Kwankwaso a Ɗaurin Auren ’Ya’yan Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

    Daga: Ibrahim Muhammad, Kano Garin Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano ya cika maƙil da dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma wajenta, yayin da…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe