Shugaban KAROTA Ya Fita Rangadin Gani Da Ido

Daga Ibrahim Muhammad

Sakamakon ƙorafe-ƙorafen al’umma da na ’yan kasuwa, Shugaban Hukuma KAROTA, Auwalu Lawan Shu’aibu Aranposu ya fita rangadin gani da ido da kansa, inda ya je mahaɗar WAPA da ke Kano, don ya gane wa idonsa yadda ake gudanar da harkokin a wajen, tare da jan kunnen masu ajiye motoci a kan hanya da masu kasa kaya a kan titi daura da ƙofar Fagge Upper Sharia Court da fakin ɗin motoci kan titin bayan kotun.

Kazalika, Shugaban Hukuma KAROTA ɗin ya leƙa Murtala Muhammad Way Kasuwar Singer har zuwa tsohuwar Bata, inda a nan ma ya samu masu kasa littattafai kan titin Bello Road da titin mai Ƙarami Plaza.

Wani abin takaici shi ne yadda mutane suka ajiye sikeli a kan titin Singa suna auna kwali da robobi da mata suna soya Awara da doya duk a kan titi, wanda hakan ba ƙaramin cutar da al’umma yake ba.

A ƙarshe Shugaban Hukuma KAROTA ya ja kunnensu, tare da gaya musu za fa a fito aiki don haka su gyara domin gwamnati ba ta son wulaƙanta kowa sai wanda ya wulaƙanta kansa domin gyaran in aka yi din al’umma za ta ji daɗi, in ji shi.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe