A Sa Dokar Hana ‘Yan Siyasa Sauya Sheƙa Daga Jam’iyyar Da Aka Zaɓe Su Sai Sun Gama Wa’adinsu -Hon. Ɗankaka Bebeji

Daga Ibrahim Muhammad

Gyaran tsarin mulki da shigar da sabbin dokoki abu ne mai kyau da ya kamata a riƙa yi lokaci-lokaci saboda abubuwa na canzawa daga wani ƙarni zuwa wani.

Hon. Ɗankaka Husaini Bebeji jigo a jam’iyyar NNPP mai bai wa Gwamnan jihar Kano shawara a ofishin mataimakin Gwamna ne ya bayyana hakan.

Ya ce abin da aka yi a ba ya watakila ba zai yiwu ba a yanzu. Ya kamata a ce ana samun lokaci ana sake tattaunawa a sake duba irin dokokin da suka daɗe dace da ba su yi daidai da zamani ba a sauya su yadda za su amfani al’umma.

Hon. Ɗankaka Husaini Bebeji ya ce yana goyon bayan matsayin gwamnatin jihar Kano kan neman ƙarin ƙananan hukumomi da jiha 100 bisa 100 domin Kano an yi yawa, kuma ba ta samun adalci da ya dace a tsarin rabon albarkatun ƙasa.

Ya yi nuni da cewa domin yanzu akwai jihohin da suka fi Kano samun kuɗaɗe na gwamnatin tarayya da ba su kai girmanta ba, idan kuwa za a sami ƙirƙiro ƙarin jiha daga cikinta za a sami cigaba.

Hon. Ɗankaka Husaini Bebeji ya ce shi yana da ra’ayin a sa doka a tsarin mulkin ƙasa ma da ya shafi ‘yan siyasa, a yi gyaran tsarin mulki a hana ‘yan siyasa sauya jam’iyyar da aka zaɓe su a ciki ba har sai sun gama wa’adinsu.

Ya ce domin bai dace a zo a zaɓi wani a jam’iyya A ko B ko C ba sannan kuma ya yi tashin gwauron zaɓi, ya koma wata. “Wannan yana koyawa mambobi da aka zaɓa musamman Musulmi cin amana shi, kuma cin amana abu ne mara kyau. Duk abin da aka ce an zaɓe ka a wata jam’iyya ya zama komai rigimar da take ciki dole ka haƙura a haka har ka gama,” in ji shi.

Hon. Ɗankaka Husaini Bebeji ya ce idan da dama ka gama za ka sake shiga zaɓe ka shiga a jam’iyyar in babu dama wasu Allah ya kawo shi ke nan don sha’anin ba nasa ba ne shi kaɗai na mutane domin Allah da ya halicci kowa ya ba shi abin da zai yi iya rayuwarsa.

  • Related Posts

    Gwamna Lawal Ya Gabatar da Kasafin Naira Biliyan 861

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya gabatar da ƙudirin kasafin kuɗi na shekarar 2026 mai darajar Naira Biliyan 861 ga Majalisar Dokokin Jihar, inda ya bayyana shi a matsayin taswirar…

    Karamci da Mutumtaƙa: Dubban Jama’a Sun Cika Garin Kwankwaso a Ɗaurin Auren ’Ya’yan Hon. Sunusi Surajo Kwankwaso

    Daga: Ibrahim Muhammad, Kano Garin Kwankwaso da ke ƙaramar hukumar Madobi a jihar Kano ya cika maƙil da dubban jama’a daga sassa daban-daban na jihar da ma wajenta, yayin da…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe