Zan Yi Koyi Da Irin Kyakkyawar Tarbiyyar Da Mahaifinmu Ya Nuna Mana -Sabon Tafidan Kano

Daga Ibrahim Muhammad

Mai Martaba Sarkin Kano, Alhaji Muhammad Sanusi ya yi naɗe-naɗen sarauta guda biyar a fadarsa, ciki har ɗansa Alhaji Adam Lamiɗo Sanusi da ka naɗa Tafidan Kano.

Tun da farko bayan naɗin, Alhaji Muhammad Sanusi ya bayyana cewa an yi wa Adam Lamiɗo Sanusi naɗin na matsayin Tafida ne a masarautar bisa la’akari da irin ƙwazo da tarbiyya da himmarsa a wajen neman ilimin addini da na zamani da ƙoƙarin kawowa al’umma cigaba.

Da yake zantawa da ‘yan jarida bayan naɗin nasa, Tafidan Kano Alhaji Adam Lamiɗo Sanusi ya gode wa Allah bisa wannan yarda.da mahaifinsa ya yi masa har aka naɗa shi wannan sarauta mai girma a masarautar Kano. Sannan ya yi fatan Allah ya ba su iko na sauke nauyin.

Ya ƙara jaddada godiya ga iyaye da masoya waɗanda suke nuna masa ƙauna har aka kai ga wannan matsayi da kuma mutane da suka zo daga wuraren daban-daban suka taya shi murna .

Haka kuma ya miƙa godiya ga Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf bisa ƙoƙarinsa na tabbatar da wannan matsayi, tare da yin addu’a gare shi da mahaifinsa Sarkin Kano. Allah ya taimake su ya biya buƙatunsu, ya karya maƙiyansu na sarari da na ɓoye.

Alhaji Adam Lamiɗo Sanusi ya ce daga cikin abubuwa da yake tsarawa akwai shiri da ake na tallafawa mutanen Kano ta ƙarƙashin wata Gidauniya da ya kafa. Sannan suna ƙoƙarin haɗa kai da gwamnatin Kano don kawo harkar lantarki da a yanzu ma batun ya yi nisa har waɗanda za su sa hannun jari sun zo Kano nan ba da jimawa ba cikin yardar Allah za a kai ga nasara.

Tafidan na Kano, Alhaji Adam Lamiɗo Sanusi ya yi alƙawarin cewa zai yi aiki tuƙuru wajen kare martabar Musulunci da masarauta da al”ummar Kano a duk inda yake, kuma zai cigaba da yin koyi da irin kyawawar tarbiyyar da mahaifinsu mai martaba Khalifa Muhammad Sanusi ya ɗora su a kai.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe