Hukumar Alhazai Ta Jihar Kano Ba Ta Mayar Da Dala 100 Ga Wasu Mahajjatan Hajjin 2023 Ba

Daga Ibrahim Muhammad, Kano

Wasu daga cikin mahajjatan da suka sauke farali a shekarar 2023 daga jihar Kano sun yi ƙorafin cewa Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano ba ta mayar musu da Dala 100 da aka cire daga guzurinsu ba, duk kuwa da cewa Hukumar Alhazai ta Ƙasa (NAHCON) ta riga ta dawo da kuɗaɗen ga mahajjatan.

Mahajjatan sun bayyana cewa tun a lokacin shirin tafiya aikin Hajji, an cire musu Dala 100 daga cikin Dala 700, inda aka ba su Dala 600, bisa dalilin kewaye da aka ce za a yi wa mahajjata sakamakon rikicin da ya ɓarke a ƙasar Sudan. Daga bisani kuma aka sanar da cewa za a dawo musu da kuɗin da aka cire.

Sun ce daga baya Hukumar Alhazai ta Jihar Kano ta umarci duk mahajjatan da abin ya shafa da su je su karɓi Dala 61,000, wanda shi ne daidai da kimar musayar Dala 100 a shekarar 2023. Sai dai, yayin da aka biya wasu daga cikinsu, har yanzu akwai da dama da ba a biya su ba.

Mahajjatan sun ƙara da cewa duk ƙoƙarin da suka yi na neman bayanin inda kuɗaɗen nasu suka tsaya daga wajen Hukumar bai haifar musu da sakamako ba. Hakan ne ya sa yanzu suke kira ga gwamnatin Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Abba Kabir Yusuf da kuma Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Kano, Lamin Ɗan Baffa, da su shiga tsakani domin bincike da kuma mayar musu da haƙƙinsu.

Sun bayyana cewa sun yi shiru na tsawon lokaci ne da fatan cewa daga bisani za a warware matsalar, sai dai ganin yadda lokaci ke wucewa ba tare da wani mataki ba, ya sa suka yanke shawarar bayyana damuwarsu a bainar jama’a.

Mahajjatan sun ce a shirye suke su bayar da dukkan haɗin kai da ake buƙata domin gudanar da sahihin bincike, domin gano inda kuɗaɗen suka maƙale, suna mai gargaɗin cewa cigaba da yin watsi da lamarin na iya janyo zargin almundahana a tafiyar da harkokin Hukumar.

  • Related Posts

    Ƙungiyar Masu Tuka Motocin Kurkura a Kano Ta Ja Hankalin Gwamnati Kan Shirin Sanya Traka Don Inganta Tsaro

    Daga Ibrahim Muhammad Ƙungiyar masu tuƙa motocin ƙurƙura da mamallakansu a jihar Kano, ta ja hankalin Gwamnati da ta yi taka-tsantsan wajen shirin dawo da tsarin sanya traka a ababen…

    Taron Ƙungiyar Masu Sayar da Abinci a Buhu: Lawan Ɓatagarawa Ya Jaddada Muhimmancin Haɗa Kai Wajen Magance Matsalar Tsaro

    Daga Ibrahim Muhammad Kano Tsohon Ministan Tsaro, Alhaji Lawan Ɓatagarawa, ya jaddada muhimmancin haɗa kai tsakanin gwamnati da kowane ɓangare na al’umma domin magance matsalar tsaro a ƙasar nan. Ɓatagarawa…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Masu Tuka Motocin Kurkura a Kano Ta Ja Hankalin Gwamnati Kan Shirin Sanya Traka Don Inganta Tsaro

    Ƙungiyar Masu Tuka Motocin Kurkura a Kano Ta Ja Hankalin Gwamnati Kan Shirin Sanya Traka Don Inganta Tsaro

    Taron Ƙungiyar Masu Sayar da Abinci a Buhu: Lawan Ɓatagarawa Ya Jaddada Muhimmancin Haɗa Kai Wajen Magance Matsalar Tsaro

    Taron Ƙungiyar Masu Sayar da Abinci a Buhu: Lawan Ɓatagarawa Ya Jaddada Muhimmancin Haɗa Kai Wajen Magance Matsalar Tsaro

    Ƙungiyar KAPAG Ta Ziyarci Shugaban Ƙaramar Hukumar Tarauni, Kano, Ta Jaddada Goyon Baya Ga APC

    Ƙungiyar KAPAG Ta Ziyarci Shugaban Ƙaramar Hukumar Tarauni, Kano, Ta Jaddada Goyon Baya Ga APC

    Asibitin Kabir Abba Dental Care da TAT Clinic And Diagnostic Sun Duba Lafiyar Sama Da Mutane 400 A Taron Zuriyar Goronduma

    Asibitin Kabir Abba Dental Care da TAT Clinic And Diagnostic Sun Duba Lafiyar Sama Da Mutane 400 A Taron Zuriyar Goronduma

    Muna Ganin Tasirin Taron Ƙarfafa Zumunci A Zuriyar Goronduma – Alhaji Habibu Umar Goronduma

    Muna Ganin Tasirin Taron Ƙarfafa Zumunci A Zuriyar Goronduma – Alhaji Habibu Umar Goronduma

    Uwar ‘Yan-Huɗu Ta Roƙi Gwamnatin Kano Taimakon Shayar Da Jariranta

    Uwar ‘Yan-Huɗu Ta Roƙi Gwamnatin Kano Taimakon Shayar Da Jariranta