Ku Guji Rikici Da Sunan Addini — Shaikh Zakzaky Ga Musulmi Da Kiristoci

Jagoran Harkar Musulunci, Shaikh Ibraheem Zakzaky ya ja hankalin musulmi da kirista a fadin kasar nan da su guji abin da zai hada su fada da sunan addini ko kabilanci.

Shehin Malamin ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karɓi baƙuncin wakilan al’ummar Unguwar Nasarawa da ke Kaduna, a wata ziyara ta musamman da ta ƙunshi manyan shugabannin addinai daga ɓangarorin Musulmi da Kiristoci a ranar Talata a gidansa dake Abuja.

Cikin tawagar akwai Mista Zakari, wakilin ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN) a ƙaramar hukumar Chikun, Alhaji Aliyu Mai Lafiya Chiroman Nasarawa, Mista Dominic, babban faston cocin Katolika na Unguwar Nasarawa, da Shaikh Alaramma Jabir Muhammad, babban limamin masallacin Juma’a na yankin.

A yayin ganawar wacce ta kasance a ranar Talata 4 ga watan Nuwamban 2025 wacce Ofishin Shehin Malamin ya labarta, Shaikh Zakzaky ya yi kira mai ƙarfi ga al’umma da su guji kowacce irin fitina ko rikici da za ta iya kawo rabuwar kai tsakanin Musulmi da Kiristoci.

Ya ce, “Kar ku yarda a haɗa ku rigima da juna, ko da da sunan addini ko da da sunan ƙabila. Ku zauna lafiya, ku haɗa kai domin amfanin kowa da kowa.”

Shehin Malamin ya bayyana cewa Kiristoci ba ‘arna’ ba ne, yana mai tunatar da cewa Allah Maɗaukaki ya ambace su a cikin Alƙur’ani da suna “Ma’abota Littafi”. Ya ce wannan dalili ne da ya wajabta a ci gaba da girmama juna da ƙarfafa zumunci da fahimtar juna a tsakanin mabiya addinan.

Wannan ganawa ta kasance wata dama ta ƙarfafa haɗin kai da fahimtar juna a tsakanin shugabannin addinai a Nasarawa, abin da da dama suka yaba da shi a matsayin mataki mai muhimmanci wajen gina zaman lafiya da haɗin kai a Kaduna da ma kasar baki ɗaya.

  • Related Posts

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a siyasar jihar Kano, kuma jagoran jam’iyyar ADC a jihar, Alhaji Ibrahim Al-Amin Little, ya bayyana rashin goyon bayansa ga yunƙurin da wasu mutane ke…

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Daga Ibrahim Muhammad An kammala bikin rufe Baje Kolin Duniya na 46 da Cibiyar Kasuwanci da Masana’antu ta Kano (KACCIMA) ta shirya, ƙarƙashin jagorancin Ambasada Usman Darma, a yammacin Asabar.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Ibrahim Little Ya Nuna Rashin Amincewa Da Yunƙurin Ganduje nlNa Kafa Hisbah Mai Zaman Kanta A Kano

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    Tinubu Ya Miƙa Lambar Karramawa Ta Ƙasa Ga Gwamna Dauda Lawal

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    An Kammala Baje Kolin Kano Na 46 Cikin Nasara

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Hukumar Kula Da Lafiya Ta Duba Lafiyar Sama Da Mutum 2,000 Da Suka Halarci Taron Baje Koli A Kano -Dakta Rahila Aliyu Muktar

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Gwamnatin Zamfara Ta Bunƙasa Harkar Kasuwanci Da Zuba Jari Da Haƙo Ma’adanai -Tafidan Maradun

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe

    Kasuwar Galadima Ta Fara Aikin Sabunta Gadar Shiga Kasuwa Da Ta Rushe