Gwamnatin Kano da Majalisa na Tafiya Lafiya Babu Saɓani -Isyaku Ali Danja

Daga Ibrahim Muhammad

Mai bai wa Gwamnan jihar Kano shawara ta musamman kan harkokin Majalisar Dokoki, Rt. Hon. Isyaku Ali Ɗanja, ya bayyana cewa gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Abba Kabir Yusuf na tafiya lafiya da Majalisar Dokokin jihar Kano, ba tare da wani rikici ko rashin fahimta ba.

Isyaku Ali Ɗanja ya ce a tsawon wannan gwamnati ba a taɓa samun wata matsala ko hayaniya tsakanin Gwamna da Majalisar Dokokin jihar Kano ba, lamarin da ke nuna kyakkyawar fahimta da mutunta juna a ɓangarorin biyu.

Ya bayyana cewa hakan ya samo asali ne sakamakon yadda Gwamna Abba Kabir Yusuf ke sauke haƙƙoƙin kowane ɓangare yadda ya kamata. “Da a ce ana tauye haƙƙoƙin ’yan majalisa, da tuni an ji koke-koke ko hayaniya,” in ji shi.

Ɗanja, wanda ya taɓa riƙe muƙamin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, tare da wakiltar ƙaramar hukumar Gazawa, ya ce Majalisar ba baƙuwa ba ce a gare shi, kasancewar ya shafe tsawon shekaru 16 yana aiki a cikinta, inda ya riƙe muƙamai daban-daban da suka haɗa da Shugaban Masu Rinjaye, Mataimakin Shugaban Majalisa, har zuwa Kakaki.

Ya ƙara da cewa a matsayinsa na mai ba Gwamna shawara, yana yin iya ƙoƙarinsa wajen tabbatar da an samu zaman lafiya da fahimta tsakanin ɓangaren zartarwa da na majalisa domin ciyar da jihar gaba.

Da yake jawabi kan biyan kuɗaɗen tsofaffin kansiloli, Ɗanja ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya cika alƙawarin da ya ɗauka na biyan tsofaffin kansilolin Gwamna Abdullahi Ganduje da ba a biya su a baya ba. Ya ce hakan ya nuna tausayi, sanin ya kamata da kuma kishin sauke nauyin da ke kansa, abin da ya sa tsofaffin kansilolin ke masa addu’a da fatan Allah Ya saka masa da alheri.

  • Related Posts

    Mai Sikeli Ya Jagoranci ‘Yan Kwankwasiyya A Nasarawa Kano, Sun Jaddada Goyon Bayansu Ga Kwankwaso

    Daga Ibrahim Muhammad Kano Jagoran Kwankwasiyya a ƙaramar hukumar Nasarawa, Kano, Alhaji Mustapha Muhammad Mai Sikeli, ya bayyana jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Dakta Rabiu Musa Kwankwaso, a matsayin mutum mai haƙuri…

    Kujerar Nasarawa A Majalisar Jihar Kano Ba Ta Sayarwa Ba Ce -Hon. MB Aliyu

    Daga Ibrahim Muhammad Kano Dan majalisar dokokin jihar Kano mai wakiltar ƙaramar hukumar Nasarawaa jihar Kano, Hon. MB Aliyu, ya bayyana cewa kujerar da yake riƙe da ita a Majalisar…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Ƙungiyar Masu Tuka Motocin Kurkura a Kano Ta Ja Hankalin Gwamnati Kan Shirin Sanya Traka Don Inganta Tsaro

    Ƙungiyar Masu Tuka Motocin Kurkura a Kano Ta Ja Hankalin Gwamnati Kan Shirin Sanya Traka Don Inganta Tsaro

    Taron Ƙungiyar Masu Sayar da Abinci a Buhu: Lawan Ɓatagarawa Ya Jaddada Muhimmancin Haɗa Kai Wajen Magance Matsalar Tsaro

    Taron Ƙungiyar Masu Sayar da Abinci a Buhu: Lawan Ɓatagarawa Ya Jaddada Muhimmancin Haɗa Kai Wajen Magance Matsalar Tsaro

    Ƙungiyar KAPAG Ta Ziyarci Shugaban Ƙaramar Hukumar Tarauni, Kano, Ta Jaddada Goyon Baya Ga APC

    Ƙungiyar KAPAG Ta Ziyarci Shugaban Ƙaramar Hukumar Tarauni, Kano, Ta Jaddada Goyon Baya Ga APC

    Asibitin Kabir Abba Dental Care da TAT Clinic And Diagnostic Sun Duba Lafiyar Sama Da Mutane 400 A Taron Zuriyar Goronduma

    Asibitin Kabir Abba Dental Care da TAT Clinic And Diagnostic Sun Duba Lafiyar Sama Da Mutane 400 A Taron Zuriyar Goronduma

    Muna Ganin Tasirin Taron Ƙarfafa Zumunci A Zuriyar Goronduma – Alhaji Habibu Umar Goronduma

    Muna Ganin Tasirin Taron Ƙarfafa Zumunci A Zuriyar Goronduma – Alhaji Habibu Umar Goronduma

    Uwar ‘Yan-Huɗu Ta Roƙi Gwamnatin Kano Taimakon Shayar Da Jariranta

    Uwar ‘Yan-Huɗu Ta Roƙi Gwamnatin Kano Taimakon Shayar Da Jariranta