Ƙungiyar Lauyoyi Reshen Ungogo Sun Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Edo

Daga Ibrahim Muhammad

Ƙungiyar Lauyoyi ta Nijeriya jihar Kano reshen Ungogo ta nuna mutuƙar damuwarta da yin Allah-wadai bisa kisan gilla da aka yi wa matafiya da suke wucewa ta garin Edo.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata takarda mai ɗauke da sa hannun shugaban ƙungiyar lauyoyi na Kano reshen Ungogo, Barusta Ahmadi Abubakar da aka raba wa manema labarai.

Ya ce wannan kusan gilla yana nuna take haƙƙin ɗan’adam na ‘yancin rayuwa cikin walwala kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasar Nijeriya ya tabbatar.

Ya yi nuni da cewa waɗannan rayuka da aka kashe na waɗanda ba su ji ba, ba su gani ba, hakan ya ci karo da kare haƙƙin ɗan’adam da tsarin rayuwa ta gari.

Ƙungiyar lauyoyin ta ƙasa Kano reshen Ungogo ta yi kira ga gwamnati a kan ta biya diyya ga iyalan waɗanda aka kashe ta, kuma tabbatar waɗanda suka aikata laifin an kama su an gabatar da su a gaban shari’a domin su girbi abin da suka aikata.

Sannan sun yi kira ga gwamnati ta samar da tsaro ga matafiya da ‘yan ƙasa ta kuma yi ƙoƙarin gano dalilai da suke jawo faruwar irin waɗannan abubuwa marasa daɗi domin a yi maganinsu.

Barista Ahmad Abubakar Gwadabe ya ce a matsayinsu na lauyoyi za su cigaba da tabbatar da ganin an kare dukkan wani haƙƙin ɗan’adam da ƙoƙarin kare haƙƙin ‘yan ƙasa ba tare da nuna bambancin ƙabila ko ɓangaranci ko bambancin addini ba.

Ƙungiyar lauyoyi ta miƙa ta’aziiyya ga iyalan mamatan da iftila’in ya rutsa da su da roƙon su zama masu haƙuri da juriya da bin doka a koyaushe.

  • Related Posts

    Rasuwar Audu Manaja Babban Rashi Ne Ga Arewa Da Nijeriya -Sulaiman Hussain

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano An bayyana rasuwar fitaccen ɗan kasuwa a harƙar man fetur, Alhaji Abdullahi Ahmad, wanda aka fi sani da Audu Manaja, a matsayin babban rashi ga Arewa…

    Asibitin Ƙashi Na Dala Ya Karrama Hon. Abba Kabir Bichi Kan Gudummawar Da Yake Bayarwa

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Asibitin Ƙashi na Tarayya da ke Dala, Kano, ya ba wa ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar Mazabar Bichi, Hon. Abba Kabir Bichi, lambar karramawa bisa gudunmawa…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Rasuwar Audu Manaja Babban Rashi Ne Ga Arewa Da Nijeriya -Sulaiman Hussain

    Rasuwar Audu Manaja Babban Rashi Ne Ga Arewa Da Nijeriya -Sulaiman Hussain

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai A ADC Reshen Kano Kan Zargin Hana Waɗanda Ba ’Yan Kwankwasiyya Ba Takara

    Sabon Rikici Ya Kunno Kai A ADC Reshen Kano Kan Zargin Hana Waɗanda Ba ’Yan Kwankwasiyya Ba Takara

    Sanata Hanga Ɗan Gwagwarmayar Siyasa Ne Mai Neman Sauyi Da Ci Gaban Al’umma – Maikarfi Dala

    Sanata Hanga Ɗan Gwagwarmayar Siyasa Ne Mai Neman Sauyi Da Ci Gaban Al’umma – Maikarfi Dala

    Asibitin Ƙashi Na Dala Ya Karrama Hon. Abba Kabir Bichi Kan Gudummawar Da Yake Bayarwa

    Asibitin Ƙashi Na Dala Ya Karrama Hon. Abba Kabir Bichi Kan Gudummawar Da Yake Bayarwa

    Gidauniyar NNPCL Ta Miƙa Na’urar MRI Ta Zamani Ga Asibitin Ƙashi Na Dala

    Gidauniyar NNPCL Ta Miƙa Na’urar MRI Ta Zamani Ga Asibitin Ƙashi Na Dala

    LEON Projects Ta Sami Lambar Karramawa Kan Aikin Gina Ɗakin MRI A Asibitin Ƙashi Na Dala

    LEON Projects Ta Sami Lambar Karramawa Kan Aikin Gina Ɗakin MRI A Asibitin Ƙashi Na Dala