ADC Jam’iyya Ce Mai Hangen Nesa Da Manufofi Na Gaskiya

Daga Ibrahim Muhammad Kano

Jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta jaddada ƙudirinta na magance matsalar rashin tsaro da ke addabar wasu sassan ƙasar nan, idan ta samu damar karɓar ragamar mulki a zaɓukan shekarar 2027.

Mataimakin Shugaban jam’iyyar ADC na ƙasa mai wakiltar shiyyar Arewa maso Yamma, Malam Jafaru Sani, ne ya bayyana hakan yayin wata ganawa da manema labarai.

Ya ce jam’iyyar ADC ta tanadi ingantattun tsare-tsare da dabaru da za su taimaka wajen shawo kan matsalar rashin tsaro a shiyyar Arewa maso Yamma da ma ƙasar nan baki ɗaya.

Haka kuma, ya bayyana cewa jam’iyyar na shirin yin muhimman gyare-gyare a ɓangaren shari’a domin tabbatar da adalci, zaman lafiya da doka ta yi aiki yadda ya kamata.

Malam Jafaru Sani ya ƙara da cewa lokaci ya yi da ‘yan Nijeriya za su rungumi sabuwar tafiya ta jam’iyyar ADC domin ceto ƙasar nan daga halin ƙunci da take ciki, inda ya danganta matsalolin da ake fuskanta da gazawar jam’iyyar mai mulki ta APC.

A cewarsa, ADC jam’iyya ce mai hangen nesa da manufofi na gaskiya, tare da shugabanni masu jajircewa da ƙwarewa, waɗanda za su iya kawo sahihin sauyi a fannonin tsaro, tattalin arziƙi da adalci.

Jam’iyyar ADC ta yi kira ga al’ummar Arewa maso Yamma da su haɗa kai da ita domin gina ƙasa mai tsaro, adalci da cigaba mai ɗorewa.

Haka kuma, ta zargi jam’iyyar APC da gazawa wajen kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Nijeriya.

  • Related Posts

    Za Mu Ci Gaba Da Ba Da Gudunmawa Wajen Tallafa Wa Matasa Kan Koyon Sana’o’in Dogaro Da Kai -Hon. Sagir Abba Fagge

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Honarabul Sagir Abba Fagge ya jaddada aniyarsa ta ci gaba da bayar da gudunmawa domin tallafa wa matasa maza da mata wajen koyon sana’o’in dogaro da…

    Ambasada Abdulrahman Salga Ya Jagoranci Gangamin Motsa Jam’iyyar ADC A Kano

    Daga Ibrahim Muhammad Kano An gudanar da wani gagarumin gangamin motsa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) tare da buɗe sabbin ofisoshin jam’iyyar a ƙaramar hukumar Dala ta jihar Kano, a…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Shirin Ceto Zamfara Na Samun Nasara, Yayin Da Gwamna Lawal Ke Duba Ayyuka A Shinkafi.

    Shirin Ceto Zamfara Na Samun Nasara, Yayin Da Gwamna Lawal Ke Duba Ayyuka A Shinkafi.

    Ma’aikatar Tsaro Na Amfani Da Ofishin NSA Wajen Gallaza Wa ’Yan Adawa – Gwamnatin Zamfara

    Ma’aikatar Tsaro Na Amfani Da Ofishin NSA Wajen Gallaza Wa ’Yan Adawa – Gwamnatin Zamfara

    The US and Great Power Politics in the Western Hemisphere: A Reinvigoration of Realism in International Relations, Geopolitics and Strategic Interest

    The US and Great Power Politics in the Western Hemisphere: A Reinvigoration of Realism in International Relations, Geopolitics and Strategic Interest

    ADC Jam’iyya Ce Mai Hangen Nesa Da Manufofi Na Gaskiya

    ADC Jam’iyya Ce Mai Hangen Nesa Da Manufofi Na Gaskiya

    Kungiyar Arewa Acquisition Skill Ta Kaddamar Da Shirin Koyar Da Mata 1,000 Sana’o’i A Fagge, Kano

    Kungiyar Arewa Acquisition Skill Ta Kaddamar Da Shirin Koyar Da Mata 1,000 Sana’o’i A Fagge, Kano

    Za Mu Ci Gaba Da Ba Da Gudunmawa Wajen Tallafa Wa Matasa Kan Koyon Sana’o’in Dogaro Da Kai -Hon. Sagir Abba Fagge

    Za Mu Ci Gaba Da Ba Da Gudunmawa Wajen Tallafa Wa Matasa Kan Koyon Sana’o’in Dogaro Da Kai -Hon. Sagir Abba Fagge