Gawuna Ya Zama Ɗan Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar NDC

Daga Ibrahim Muhammad, Kano

Jam’iyyar National NDC ta bayyana tsohon ɗan takar gwamnan Kano kuma tsohon mataimakin gwamnan jihar, Dakta Nasiru Yusuf Gawuna, a matsayin ɗan takararta na kujerar Sanatan Kano ta Tsakiya domin zaɓen shekarar 2027.

Sanarwar ta biyo bayan wata da jam’iyyar ta sanar da Comrade Aminu Abdussalam Gwarzo a matsayin ɗan takar gwamnan Kano. Rahotanni sun nuna cewa zaɓen Gawuna ya samu ne bayan doguwar tattaunawa da shawarwari tsakanin jagororin jam’iyyar da masu ruwa da tsaki a jihar.

Manufar wannan mataki, a cewar masu sharhi, shi ne ƙarfafa haɗin kai a cikin jam’iyyar da kuma shirya kyakkyawar dabara wajen tunkar zaɓe mai zuwa.

Masu nazarin siyasa na kallon nadin Gawuna a matsayin muhimmin sauyi a siyasar Kano, musamman ganin kwarewarsa da gogewarsa a gwamnati. Tsohon mataimakin gwamnan ya taba rike muƙamai da dama ciki har da kwamishinan noma da kuma shugaban karamar hukumar Nassarawa.

Jam’iyyar NDC ta ce tana ci gaba da bayyana ’yan takararta na muƙamai daban-daban a matakin jiha da na ƙasa, yayin da shirye-shiryen zaɓen 2027 ke ƙara ƙarfi.

  • Related Posts

    Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

    Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana shirinta na tallafa wa mata, ’yan mata, masu nakasa da sauran marasa galihu sama da miliyan daya a faɗin jihar, a wani mataki da ta…

    BOMBOY: Nasarar Samun Tikitin Takara Ba Tare Da Hamayya Ba Ta Gwamna Abba Da Hassan Hussain Ta Nuna Gamsuwar Al’umma

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jigo a jam’iyyar APC kuma ɗaya daga cikin hadiman tafiyar siyasar Hon. Hassan Shehu Hussain, ɗan majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar ƙaramar hukumar Nasarawa, Hon.…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Dan’iya mourns attack victims, urges decisive action against insecurity

    Dan’iya mourns attack victims, urges decisive action against insecurity

    Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

    Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

    BOMBOY: Nasarar Samun Tikitin Takara Ba Tare Da Hamayya Ba Ta Gwamna Abba Da Hassan Hussain Ta Nuna Gamsuwar Al’umma

    BOMBOY: Nasarar Samun Tikitin Takara Ba Tare Da Hamayya Ba Ta Gwamna Abba Da Hassan Hussain Ta Nuna Gamsuwar Al’umma

    Nasarar Atiku A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Na ADC, Nasara Ce Ga Masu Kishin Ci Gaban Ƙasa -Ambasada Mainasara Salga

    Nasarar Atiku A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Na ADC, Nasara Ce Ga Masu Kishin Ci Gaban Ƙasa -Ambasada Mainasara Salga

    Gawuna Ya Zama Ɗan Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar NDC

    Gawuna Ya Zama Ɗan Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar NDC

    Sarkin Margunawan Kano Ya Taya Musulmi Murnar Sallah Ya Yi Kira Ga Kyautata Haɗin Kai Da Zaman Lafiya

    Sarkin Margunawan Kano Ya Taya Musulmi Murnar Sallah Ya Yi Kira Ga Kyautata Haɗin Kai Da Zaman Lafiya