APC Ta Amince Da Gwamna Lawal Domin Takarar Wa’adi Na Biyu A Zamfara

Jam’iyyar APC ta tantance tare da amincewa da Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, domin sake tsayawa takarar gwamna a zaɓen shekarar 2027.

Kwamitin tantance ’yan takarar na jam’iyyar mai mulki ƙarƙashin jagorancin Shugaban APC na ƙasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ne ya tantance gwamnan a Abuja ranar Juma’a.

Tun a ranar Talata 5 ga watan Mayun 2026, wata tawaga ƙarƙashin jagorancin Sakataren Gwamnatin Jihar Zamfara, Abubakar Nakwada, ta miƙa cikakkun fom ɗin nuna sha’awa da tsayawa takara na Gwamna Dauda Lawal ga kwamitin tantancewa na APC a Abuja.

Tun da farko dai masu ruwa da tsaki na APC a jihar Zamfara sun amince da Gwamna Dauda Lawal a matsayin ɗan takara guda tilo na jam’iyyar domin kujerar gwamna.

An cimma wannan matsaya ne a wani babban taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar ranar 25 ga watan Afrilun 2026 a gidan gwamnatin jihar da ke Gusau, babban birnin Zamfara.

A yayin taron, shugabannin jam’iyyar sun kuma bayyana goyon bayansu ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu domin sake neman wa’adi na biyu a babban zaɓen shekarar 2027.

Taron ya haɗa manyan jagororin APC daga sassa daban-daban na jihar, ciki har da tsoffin gwamnonin Zamfara guda huɗu; Ahmed Sani Yarima, Mahmuda Aliyu Shinkafi, Abdulaziz Yari da Bello Mohammed Matawalle.

Haka kuma, manyan jami’an gwamnati da aka zaɓa, dattawan jam’iyya, da wakilan matasa da mata daga faɗin jihar sun halarci taron.

Matakin amincewa da Gwamna Dauda Lawal na zuwa ne yayin da shirye-shiryen siyasa gabanin zaɓen 2027 ke ci gaba da ɗaukar zafi a sassa daban-daban na ƙasar nan.

Related Posts

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayyana shirinta na tallafa wa mata, ’yan mata, masu nakasa da sauran marasa galihu sama da miliyan daya a faɗin jihar, a wani mataki da ta…

Gwamnan Zamfara Ya Buƙaci A Ƙara Addu’o’in Zaman Lafiya Yayin Bikin Babbar Sallah

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya yi kira ga al’ummar jihar da ma ɗaukacin Nijeriya da su ƙara dagewa wajen yin addu’o’in zaman lafiya da tsaro a yayin bikin Babbar…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Dan’iya mourns attack victims, urges decisive action against insecurity

Dan’iya mourns attack victims, urges decisive action against insecurity

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

BOMBOY: Nasarar Samun Tikitin Takara Ba Tare Da Hamayya Ba Ta Gwamna Abba Da Hassan Hussain Ta Nuna Gamsuwar Al’umma

BOMBOY: Nasarar Samun Tikitin Takara Ba Tare Da Hamayya Ba Ta Gwamna Abba Da Hassan Hussain Ta Nuna Gamsuwar Al’umma

Nasarar Atiku A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Na ADC, Nasara Ce Ga Masu Kishin Ci Gaban Ƙasa -Ambasada Mainasara Salga

Nasarar Atiku A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Na ADC, Nasara Ce Ga Masu Kishin Ci Gaban Ƙasa -Ambasada Mainasara Salga

Gawuna Ya Zama Ɗan Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar NDC

Gawuna Ya Zama Ɗan Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar NDC

Sarkin Margunawan Kano Ya Taya Musulmi Murnar Sallah Ya Yi Kira Ga Kyautata Haɗin Kai Da Zaman Lafiya

Sarkin Margunawan Kano Ya Taya Musulmi Murnar Sallah Ya Yi Kira Ga Kyautata Haɗin Kai Da Zaman Lafiya