Daga Ibrahim Muhammad, Kano
Sabon Ajiyan Kano, Alhaji Muhammad Sunusi Bello, wanda Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II ya naɗa a fadarsa ranar Juma’a, ya bayyana cewa naɗin da aka yi masa wata babbar karramawa ce da aka yi masa bisa yarda da amincewa da shi.
Da yake zantawa da manema labarai bayan naɗin, ya ce farin cikinsa ba zai misaltu ba, musamman idan aka yi la’akari da irin kalaman yabo da hujjojin da Sarkin ya bayyana game da shi yayin bikin naɗin.
Ya ce duk wanda ya halarci bikin naɗin zai fahimci irin karramawar da aka yi masa, domin kalaman da Sarkin ya yi sun nuna gamsuwa da cancantarsa, abin da ya ƙara masa farin ciki fiye da sarautar kanta.
Sabon Ajiyan Kanon ya ƙara da cewa, a cikin hakiman Kano da yawansu ya kai kusan 74, Sarkin ya zaɓe shi ya ba shi wannan sarauta, wanda ya bayyana a matsayin babbar nasara da ba zai iya bayyana ta da baki ba.
Ya ce abin da ya rage musu shi ne ci gaba da yi wa Sarkin addu’a, yana roƙon Allah Ya tsare mutuncinsa, Ya ƙara masa lafiya, nasara da kuma tsawon rai.
Har ila yau, ya bayyana cewa sarautar “Ajiya” ba a ba ta sai ga wanda aka amince da shi, yana mai cewa duk wanda Sarkin Kano ya ba wannan mukami, to yana nuni da cewa an yarda da gaskiyarsa, amincinsa da kuma rikon amanarsa.
Dangane da tarihin sarautar, Alhaji Muhammad Sunusi Bello ya ce a da ba a da wannan sarauta a Kano, sai a zamanin marigayi Sarkin Kano, Ado Bayero ne aka fara ƙirƙiro ta, inda aka fara naɗa Alhaji Muhammadu Ɗansarari, bayan rasuwarsa sai ɗansa Aminu Ɗansarari ya gaje shi. Daga bisani kuma aka naɗa Ja’afar Shanono, kafin yanzu da aka naɗa shi a matsayin Ajiyan Kano na huɗu a tarihin sarautar.







