Daga Ibrahim Muhammad, Kano
An gudanar da zaɓen fid-da-gwani na neman tsayawa takarar kujerar majalisar tarayya ta ƙaramar hukumar Dala a jihar Kano a ƙarƙashin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) a ranar 21 ga Mayu, 2026.
Zaɓen ya gudana ne bisa tsarin “ƙato bayan ƙato” kamar yadda dokar Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta tanada, inda aka bayyana cewa an gudanar da shi cikin lumana da kwanciyar hankali.
’Yan takara uku ne suka fafata a zaɓen, waɗanda suka haɗa da Hon. Abdurrahman Mansur Mainasara Salga, Hon. Nasir Isa da Hon. Bashir Muhammad.
An gudanar da zaɓen ne ƙarƙashin kulawar wakilan uwar jam’iyyar ADC ta ƙasa, ƙungiyoyin sa ido da jami’an tsaro, yayin da mambobin jam’iyyar maza da mata suka fito domin kaɗa ƙuri’unsu.
Bayan kammala zaɓen, kwamitin gudanarwa ya bayyana sakamakon kamar haka: Hon. Nasir Isa ya samu ƙuri’u 821, Hon. Bashir Muhammad ya samu ƙuri’u 1,584, yayin da Hon. Amb. Abdurrahman Mansur Mainasara Salga ya samu ƙuri’u 8,973.
Jimillar ƙuri’un da aka kaɗa sun kai 11,377.
Bisa ga wannan sakamako, an bayyana Hon. Amb. Abdurrahman Mansur Mainasara Salga a matsayin wanda ya lashe zaɓen fidda gwani na jam’iyyar ADC domin tsayawa takarar kujerar majalisar tarayya ta Dala a zaɓen shekarar 2027.
Da yake magana bayan ayyana sakamakon zaɓen, Hon. Abdurrahman Mainasara Salga ya bayyana farin cikinsa kan nasarar da ya samu, inda ya danganta hakan da goyon bayan da mambobin jam’iyyar ADC a Dala suka ba shi.
Ya kuma yi kira ga sauran ’yan takarar da suka fafata da shi da su haɗa kai domin mara wa jam’iyyar ADC baya, domin tabbatar da nasararta a zaɓen 2027.






