Daga Ibrahim Muhammad Kano
Al’ummar ƙananan hukumomi 15 da ke mazaɓar Kano ta Tsakiya sun yi kira ga Shugaban Matasan Jam’iyyar ADC na ƙasa, Hon. Balarabe Rufa’i Soronɗinki, da ya fito takarar Sanatan Kano ta Tsakiya a zaɓen shekarar 2027.
Masu kiran sun bayyana Balarabe Rufa’i Soronɗinki a matsayin matashi mai nagarta, kishin al’umma da kuma jajircewa wajen kawo ci gaba daga tushe.
Sun ce sun gamsu da irin ƙwazonsa da sadaukarwarsa wajen tabbatar da an samu sauyi mai amfani ga al’umma, tare da bayyana cewa tsayawarsa takara zai taimaka wajen samar da ci gaba mai dorewa a mazabar Kano ta Tsakiya.
Haka kuma, sun yabawa rawar da yake takawa a jam’iyyar ADC, musamman wajen bai wa matasa dama a harkokin siyasa da kuma ƙoƙarinsa na bunƙasa jam’iyyar ba tare da gajiyawa ba.
A cewarsu, irin gudunmawar da yake bayarwa ga jam’iyyar da al’umma ya nuna cewa ya cancanci wakiltar Kano ta Tsakiya a Majalisar Dattawa.
Masu ruwa da tsaki na ADC a Kano ta Tsakiya sun kara da cewa lokaci ya yi da Balarabe Soronɗinki zai amsa kiran al’umma domin tsayawa takarar kujerar Sanata.
“Jam’iyyar ADC ta bayyana aniyarta ta bai wa matasa damar tsayawa takarar kujerar Sanata a kowace jiha, kuma a Kano ta Tsakiya, Balarabe Rufa’i Soronɗinki ne zaɓin al’umma. Muna kira gare shi da ya amsa wannan kira,” in ji su.






