An Yaba Da Wakilcin Hon. Sani Adamu Wakili A Ungogo Da Minjibir, An Nemi A Sake Tsayar Da Shi A 2027

Daga Ibrahim Muhammad, Kano

Al’ummar ƙananan hukumomin Ungogo da Minjibir a jihar kano sun bayyana gamsuwarsu da wakilcin da Hon. Sani Adamu Wakili ke yi musu a Majalisar Tarayya, tare da kira ga jam’iyyar NDC da ta sake tsayar da shi takara a zaɓen 2027.

Wani mazaunin unguwar ‘Yar’adua da ke ƙaramar hukumar Ungogo, Alhaji Ibrahim Usman Ali Meshelia, ne ya bayyana hakan yayin da yake yabawa irin ayyukan ci gaban da ɗan majalisar ke aiwatarwa a yankunan biyu.

Ya ce tun bayan kafuwar mazaɓar Ungogo da Minjibir, ba a taɓa samun wakilin da ya kawo sauye-sauye da tallafi ga al’umma kamar Hon. Sani Adamu Wakili ba.

A cewarsa, ɗan majalisar ya taimaka wa matasa da dama ta hanyar rabon motoci, babura da Adaidaita Sahu kyauta domin rage rashin aikin yi da bunƙasa sana’o’i.

Haka kuma, ya ce Hon. Sani Adamu Wakili ya bai wa mata tallafin jari domin fara ƙananan sana’o’i, abin da ya bayyana a matsayin wani babban ci gaba ga rayuwar iyalai a yankin.

Meshelia ya ƙara da cewa ɗan majalisar na bayar da muhimmanci sosai ga harkar ilimi, inda yake ɗaukar nauyin karatun ɗalibai a makarantun kimiyya da sauran manyan makarantu.

Ya kuma bayyana cewa a lokutan Azumi da bukukuwan Sallah, Hon. Sani Adamu Wakili kan raba kayan abinci da tallafin kuɗi ga al’umma a faɗin Ungogo da Minjibir.
“Mutanen Ungogo da Minjibir suna goyon bayan Hon. Sani Adamu Wakili kashi 100 bisa 100, kuma muna ci gaba da bin tafarkin jagorancin Dr. Rabiu Musa Kwankwaso a ƙarƙashin jam’iyyar NDC,” in ji shi.

Ya ce ɗan majalisar mutum ne mai sauraron koke-koken jama’a, inda ya bayyana cewa kofarsa a buɗe take domin karɓar baƙi da sauraron matsalolin al’umma a kowane lokaci.

Kazalika, ya ce Hon. Sani Adamu Wakili na gabatar da kudurori da ayyukan ci gaba da suka haɗa da gina hanyoyi da samar da fitilun hasken rana a yankuna da dama na Ungogo da Minjibir.

“Yanzu idan ka shiga wasu sassan yankin da dare, za ka ga tamkar da rana ne saboda hasken fitilun da aka girka,” in ji Meshelia.

A ƙarshe, ya yi kira ga al’ummar Ungogo da Minjibir da su ci gaba da mara wa Hon. Sani Adamu Wakili baya tare da sake zaɓensa a ƙarƙashin jam’iyyar NDC a shekarar 2027 domin ci gaba da ayyukan raya yankin.

  • Related Posts

    Sulhu Ya Samu: ATM Gwarzo Ya Janye Wa Barau A Takarar Sanata A APC Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jagoran Jam’iyyar APC a Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci wani zama na sulhu da ya haɗa manyan jiga-jigan jam’iyyar biyu daga Kano ta Arewa,…

    Daga Dokajin Kano Zuwa Sarkin Sudan: Abin Farin Ciki Ne -Injiniya Aminu Aliyu Wudil

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Injiniya Aminu Aliyu Wudil, Wamban Sarkin Sudan na Kano, ya bayyana farin cikinsa bisa naɗin Alhaji Muhammad Aliyu Wudil a matsayin Sarkin Sudan na Kano, wanda…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Dan’iya mourns attack victims, urges decisive action against insecurity

    Dan’iya mourns attack victims, urges decisive action against insecurity

    Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

    Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

    BOMBOY: Nasarar Samun Tikitin Takara Ba Tare Da Hamayya Ba Ta Gwamna Abba Da Hassan Hussain Ta Nuna Gamsuwar Al’umma

    BOMBOY: Nasarar Samun Tikitin Takara Ba Tare Da Hamayya Ba Ta Gwamna Abba Da Hassan Hussain Ta Nuna Gamsuwar Al’umma

    Nasarar Atiku A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Na ADC, Nasara Ce Ga Masu Kishin Ci Gaban Ƙasa -Ambasada Mainasara Salga

    Nasarar Atiku A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Na ADC, Nasara Ce Ga Masu Kishin Ci Gaban Ƙasa -Ambasada Mainasara Salga

    Gawuna Ya Zama Ɗan Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar NDC

    Gawuna Ya Zama Ɗan Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar NDC

    Sarkin Margunawan Kano Ya Taya Musulmi Murnar Sallah Ya Yi Kira Ga Kyautata Haɗin Kai Da Zaman Lafiya

    Sarkin Margunawan Kano Ya Taya Musulmi Murnar Sallah Ya Yi Kira Ga Kyautata Haɗin Kai Da Zaman Lafiya