Daga Ibrahim Muhammad Kano
Gwamnatin jihar Kano ƙarƙashin jagorancin Injiniya Abba Kabir Yusuf ta ƙaryata Rahoto dak yawa na cewa ana shirin tsige Sarkin Kano, Malam Muhammadu Sanusi II sakamakon sauyin jam’iyya da Gwamnan Abba ya yi zuwa jam’iyyar APC.
Sanusi Bature Dawakin Tofa mai magana da yawun Gwamnan jihar Kano ne ya bayyana hakan ya ce babu wani shiri ko yarjejeniya da zai kai ga tsige Sarki Sanusi.
Ya yi nuni da cewa: “An naɗa Sarki Malam Muhammad Sanusi ne bisa doka bayan soke dokar masarautu, kuma babu wani shiri a matakin zartarwa na yin wani ƙarin gyaran.”
Ya tabbatar da cewa komawar Gwamna zuwa APC ba zai sauya halin da ake ciki ba ko kaɗan. “Sarki Sanusi zai cigaba da zama Sarkin Kano, babu wata niyya ta maye gurbinsa,” in ji shi.
Ya bayyana rahotannin da ke zagawa a matsayin jita-jita marasa tushe da mutane ba sa fatan alheri ga Jihar Kano ke haɗawa.
Sanusi Bature Dawakin Tofa ya yi kira ga al’ummar jihar Kano su yi watsi jita-jitar, sannan su gujewa yaɗa labarai marasa tushe.






