Jam’iyyar NNPP Ta Koka Kan Zargin Musgunawa Da Gwamnatin Jihar Kano Ke Yi Wa Mambobinta

Daga Ibrahim Muhammad Kano

Jam’iyyar NNPP ta zargi gwamnatin jihar Kano da ƙoƙarin musgunawa mambobinta, bisa zargin cewa ana ɗaukar matakai a kansu ne saboda sun ƙi amincewa su bi gwamnatin zuwa wata jam’iyya.

Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na jam’iyyar a jihar, Injiniya Ibrahim Ƙaraye ya fitar, inda ya bayyana damuwar jam’iyyar kan wasu matakai da ta ce ba su dace da tsarin dimokuraɗiyya ba.

Jam’iyyar ta ce gwamnatin jihar Kano an zaɓe ta ne ƙarƙashin tutar NNPP, kafin daga bisani ta yi watsi da jam’iyyar, tare da komawa jam’iyyar APC.

Ta ƙara da cewa daga nan ne aka fara ɗaukar matakan da suka haɗa da janye kujerun aikin Hajji da aka ware wa wasu daga cikin mambobinta, ciki har da tsofaffin kwamishinoni, masu ba gwamnati shawara da kuma wasu shugabannin jam’iyya.

A cewar Ƙaraye, mutanen da abin ya shafa a matsayinsu na ‘yan jihar Kano suna da cikakken haƙƙin cin gajiyar irin waɗannan damammaki kamar yadda sauran al’umma ke yi.

Jam’iyyar ta kuma zargi gwamnatin da matsa lamba da tsoratar da tsofaffin masu riƙe da muƙaman siyasa domin su mayar da motocin gwamnati da aka ba su lokacin da suke kan aiki, tana mai cewa motocin na daga cikin haƙƙoƙin da aka tanadar musu bisa hidimar da suka yi wa al’umma.

NNPP ta buƙaci gwamnatin jihar da ta dakatar da duk wasu matakai da ka iya tauye ko raunana ginshiƙan dimokuraɗiyya, tare da jaddada buƙatar gudanar da siyasa cikin mutunta juna da bin doka.

  • Related Posts

    Mataimakiyar Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya Ta Jinjina Wa Gwamnan Zamfara

    Mataimakiyar Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya, Amina Mohammed, ta bayyana cewa Jihar Zamfara yanzu ta zama mai sauƙin isa ga masu zuba jari da abokan hulɗa, tare da jaddada cewa…

    Al’ummar Kano Ta Arewa Sun Yi Gangamin Neman Gwarzo Ya Fito Takarar Sanata

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Al’ummar yankin Kano ta Arewa sun gudanar da wani gangami domin nuna buƙatarsu ga Injiniya Abdullahi Tijjani Muhammad Gwarzo da ya fito takarar sanatan yankin a…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Shugaban NASEMA, Akwash, Ya Bayyana Ayyukan Shekara Daya

    Shugaban NASEMA, Akwash, Ya Bayyana Ayyukan Shekara Daya

    Sanya Bukatun Kano A Gaba Zai Haɗa Kan Jama’a -Bala Muhammad Gwagwarwa

    Sanya Bukatun Kano A Gaba Zai Haɗa Kan Jama’a -Bala Muhammad Gwagwarwa

    ‘Ana Zargin Yunƙurin Ɓata Sunan Tsohon Mataimakin Gwamnan Kano’

    ‘Ana Zargin Yunƙurin Ɓata Sunan Tsohon Mataimakin Gwamnan Kano’

    Karramawar Da Aka Yi Min Sakamakon Kyakkyawar Tarbiyya Ce Daga Iyayena -Amb. Dakta Nana Maryam Gwambe

    Karramawar Da Aka Yi Min Sakamakon Kyakkyawar Tarbiyya Ce Daga Iyayena -Amb. Dakta Nana Maryam Gwambe

    DSS Ta Saki Jami’an Gwamnatin Kano Kan Zargin Ɓata Sunan Kwankwaso

    DSS Ta Saki Jami’an Gwamnatin Kano Kan Zargin Ɓata Sunan Kwankwaso

    HARIN TA’ADDANCI A BUKKUYUM: Gwamna Lawal Ya Bayyana Shi Da Aikin Rashin Imani

    HARIN TA’ADDANCI A BUKKUYUM: Gwamna Lawal Ya Bayyana Shi Da Aikin Rashin Imani