HARIN TA’ADDANCI A BUKKUYUM: Gwamna Lawal Ya Bayyana Shi Da Aikin Rashin Imani

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana matuƙar alhini da jimami kan mummunan harin da ’yan bindiga suka kai a wasu ƙauyuka na Ƙaramar Hukumar Bukkuyum, wanda ya yi sanadin salwantar rayukan bayin Allah tare da jikkata wasu da dama.

Gwamnan ya bayyana harin da aka kai da dare a ƙauyukan Bunkasau, Yar Galma (Unguwar Zarumai) da kuma Dogon Daji (Unguwar Adabka) a matsayin mummunan aiki na tashin hankali da rashin tausayi, wanda aka aikata kan fararen hula marasa kariya.

Ya kuma miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda suka rasa ’yan uwansu, yana mai nuna alhini da jimami tare da su a wannan lokaci na babban rashi da baƙin ciki.

A wani mataki na gaggawa, Gwamna Lawal ya umarci a tura wata babbar tawaga ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Gwamna domin kai saƙon jaje, tallafa wa iyalan da abin ya shafa, tare da tabbatar da cewa waɗanda suka jikkata sun samu kulawar lafiya cikin gaggawa.

Haka kuma, ya tabbatar wa al’ummar jihar Zamfara cewa gwamnatinsa za ta ƙara zage damtse wajen kare rayuka da dukiyoyi, tare da ɗaukar matakai masu ƙarfi domin dawo da zaman lafiya a dukkan sassan jihar.

SULAIMAN BALA IDRIS
Mai Magana da Yawun Gwamnan Jihar Zamfara
Afrilu 12, 2026

Related Posts

Shugaban NASEMA, Akwash, Ya Bayyana Ayyukan Shekara Daya

Daga Zubairu Lawal Babban Darakta Janar na NASEMA, Barrista Benjamin Akwash, ya gabatar da rahoton ayyukan shekara guda a Lafia, inda ya bayyana nasarori da kalubalen da hukumar ta fuskanta.…

Karramawar Da Aka Yi Min Sakamakon Kyakkyawar Tarbiyya Ce Daga Iyayena -Amb. Dakta Nana Maryam Gwambe

Daga Ibrahim Muhammad Kano Ƙungiyar WAZOBIA Conflicts Resolution and Peace Advocacy Initiative (WARCOPIA), ƙarƙashin jagorancin Ambasada Garba Sulaiman Marafa (Marafan Lagos), ta gudanar da taron karrama wasu zaɓaɓɓun mutane da…

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You Missed

Shugaban NASEMA, Akwash, Ya Bayyana Ayyukan Shekara Daya

Shugaban NASEMA, Akwash, Ya Bayyana Ayyukan Shekara Daya

Sanya Bukatun Kano A Gaba Zai Haɗa Kan Jama’a -Bala Muhammad Gwagwarwa

Sanya Bukatun Kano A Gaba Zai Haɗa Kan Jama’a -Bala Muhammad Gwagwarwa

‘Ana Zargin Yunƙurin Ɓata Sunan Tsohon Mataimakin Gwamnan Kano’

‘Ana Zargin Yunƙurin Ɓata Sunan Tsohon Mataimakin Gwamnan Kano’

Karramawar Da Aka Yi Min Sakamakon Kyakkyawar Tarbiyya Ce Daga Iyayena -Amb. Dakta Nana Maryam Gwambe

Karramawar Da Aka Yi Min Sakamakon Kyakkyawar Tarbiyya Ce Daga Iyayena -Amb. Dakta Nana Maryam Gwambe

DSS Ta Saki Jami’an Gwamnatin Kano Kan Zargin Ɓata Sunan Kwankwaso

DSS Ta Saki Jami’an Gwamnatin Kano Kan Zargin Ɓata Sunan Kwankwaso

HARIN TA’ADDANCI A BUKKUYUM: Gwamna Lawal Ya Bayyana Shi Da Aikin Rashin Imani

HARIN TA’ADDANCI A BUKKUYUM: Gwamna Lawal Ya Bayyana Shi Da Aikin Rashin Imani