Za Mu Ba Gwamna Abba Kabir Yusuf Cikakken Goyon Baya -Hon. Ado Tati

Daga Ibrahim Muhammad, Kano

Jigo a jam’iyyar APC kuma Shugaban Jami’ar Siyasa ta Gangariya na ƙasa, Hon. Ado Tati, ya bayyana aniyarsa ta ba Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf, cikakken goyon baya da gudunmawa domin bunƙasa ci gaban jihar Kano.

Hon. Ado Tati ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan karɓar Gwamna Abba Kabir Yusuf, wanda ya koma jam’iyyar APC a ranar Litinin.

Ya ce ya yi matuƙar farin ciki tare da gode wa Allah da Ya nuna musu ranar da suka sake haɗuwa a tafiyar siyasa, yana mai bayyana cewa tun da daɗewa akwai kyakkyawar alaƙar aminci tsakaninsa da Gwamna Abba Kabir Yusuf.

“Ni da Gwamna Abba Kabir Yusuf muna da tsohuwar alaƙa ta aminci. Ba mu taɓa rabuwa da juna ba a mu’amala. Mutum ne mai sanin ya kamata, hangen nesa da girmama mutane,” in ji shi.

Hon. Ado Tati ya ƙara da cewa sake haɗuwarsu a tafiyar siyasa wata dama ce da za ta ƙara ƙarfafa haɗin kai, inda ya jaddada cewa zai ba gwamnan dukkan goyon baya da gudunmawar da ta dace domin ganin an samu cigaba mai ɗorewa a jihar Kano a ƙarƙashin wannan gwamnati.

Ya bayyana Gwamna Abba Kabir Yusuf a matsayin shugaba nagari mai aiki tuƙuru, kishin al’umma da siyasar fahimta, yana mai cewa dawowarsa jam’iyyar APC zai ƙara ba shi damar gina Kano, tare da haɗa kan al’ummar jihar baki ɗaya.

  • Related Posts

    Shugaban NASEMA, Akwash, Ya Bayyana Ayyukan Shekara Daya

    Daga Zubairu Lawal Babban Darakta Janar na NASEMA, Barrista Benjamin Akwash, ya gabatar da rahoton ayyukan shekara guda a Lafia, inda ya bayyana nasarori da kalubalen da hukumar ta fuskanta.…

    Karramawar Da Aka Yi Min Sakamakon Kyakkyawar Tarbiyya Ce Daga Iyayena -Amb. Dakta Nana Maryam Gwambe

    Daga Ibrahim Muhammad Kano Ƙungiyar WAZOBIA Conflicts Resolution and Peace Advocacy Initiative (WARCOPIA), ƙarƙashin jagorancin Ambasada Garba Sulaiman Marafa (Marafan Lagos), ta gudanar da taron karrama wasu zaɓaɓɓun mutane da…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Shugaban NASEMA, Akwash, Ya Bayyana Ayyukan Shekara Daya

    Shugaban NASEMA, Akwash, Ya Bayyana Ayyukan Shekara Daya

    Sanya Bukatun Kano A Gaba Zai Haɗa Kan Jama’a -Bala Muhammad Gwagwarwa

    Sanya Bukatun Kano A Gaba Zai Haɗa Kan Jama’a -Bala Muhammad Gwagwarwa

    ‘Ana Zargin Yunƙurin Ɓata Sunan Tsohon Mataimakin Gwamnan Kano’

    ‘Ana Zargin Yunƙurin Ɓata Sunan Tsohon Mataimakin Gwamnan Kano’

    Karramawar Da Aka Yi Min Sakamakon Kyakkyawar Tarbiyya Ce Daga Iyayena -Amb. Dakta Nana Maryam Gwambe

    Karramawar Da Aka Yi Min Sakamakon Kyakkyawar Tarbiyya Ce Daga Iyayena -Amb. Dakta Nana Maryam Gwambe

    DSS Ta Saki Jami’an Gwamnatin Kano Kan Zargin Ɓata Sunan Kwankwaso

    DSS Ta Saki Jami’an Gwamnatin Kano Kan Zargin Ɓata Sunan Kwankwaso

    HARIN TA’ADDANCI A BUKKUYUM: Gwamna Lawal Ya Bayyana Shi Da Aikin Rashin Imani

    HARIN TA’ADDANCI A BUKKUYUM: Gwamna Lawal Ya Bayyana Shi Da Aikin Rashin Imani