Daga Ibrahim Muhammad Kano
Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Ƙasa kan Harkokin Yaɗa Labarai, Malam Abdul’aziz Abdul’aziz, ya wakilci Shugaban Ƙasa Asiwaju Bola Ahmed Tinubu wajen kai ziyarar ta’aziyya ga iyalan Malam Haruna, wanda aka yi wa matarsa da ’ya’yansa kisan gilla a jihar Kano.
A yayin ziyarar, Malam Abdul’aziz ya miƙa saƙon ta’aziyyar Shugaban Ƙasa ga iyalan marigayan, tare da nuna alhini da Allah wadai da wannan mummunan lamari.
Ya kuma tabbatar musu da cewa Shugaban Ƙasa ya bayar da umarni na musamman ga hukumomin tsaro domin gaggauta bincike tare da tabbatar da hukunta duk wanda aka samu da hannu a aikata wannan ta’asa, kamar yadda dokar ƙasa ta tanada.
Haka kuma, Malam Abdul’aziz ya kai wata ziyarar ta’aziyya dangane da rasuwar Bature Abdulaziz, wanda Allah ya yi wa rasuwa kwanaki uku da suka gabata.
A ziyarar, ya miƙa ta’aziyya ga iyalai, ’yan uwa da abokan arziƙi a madadin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu.
Ya yi addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki ya ji ƙan marigayin da sauran mamatan, ya gafarta musu, tare da bai wa iyalansu haƙurin jure wannan babban rashi.






