Daga Ibrahim Muhammad, Kano
An bayyana cewa an samu gagarumin zaman lafiya da haɗin kai a tsakanin al’ummomi da ƙabilu mabambanta da ke zaune a garin Gama, da ke ƙaramar hukumar Nasarawa a jihar Kano ne sakamakon kyakkyawan jagorancin Dagacin Gama, Alhaji Rabiu Isyaku, tun bayan naɗa shi shekaru 25 da suka gabata.
Mai Unguwar Gwagwarwa, kuma maƙoci ga Dagacin Gama, Alhaji Yusuf Adamu Bello, ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da ’yan jarida a taron bikin cikar Dagacin Gama shekaru 25 a kan mulki.
Ya ce dukkan ƙabilun da ke zaune a yankin suna rayuwa cikin fahimta da mutunta juna, inda Dagacin ya rungume su tare da nuna musu muhimmancin zaman lafiya da haɗin kai, lamarin da ya sa ba su da wata fargaba a zamantakewarsu.
A cewarsa, “Dagacin Gama shugaba ne mai girmama jama’a da kula da zumunci. Idan wani al’amari ya taso, ko na farin ciki ko na akasin haka, zai zo da kansa ya taya ka murna ko alhini.”
Mai Unguwar ya ƙara da yi wa Dagacin Gama fatan alheri tare da addu’ar Allah Ya saka masa da alheri bisa irin nasarorin da ya samu a cikin waɗannan shekaru 25, tare da roƙon Allah Ya ƙara masa ƙarfi da nasara a gaba.
Haka kuma, ya yi addu’ar Allah Ya bai wa al’ummar yankin Gama, ƙaramar hukumar Nasarawa da ma jihar Kano baki ɗaya zaman lafiya mai ɗorewa.
Alhaji Yusuf Adamu Bello ya jaddada cewa al’ummar yankin suna ba Dagacin Gama da dukkan masu unguwannin da ke ƙarƙashinsa cikakken goyon baya da biyayya, bisa kyakkyawan shugabancin da suke gani a aikace.






