An Raba Wa Jama’a Kayan Abinci A Maulidi A Potiskum

Daga Yusuf Wali

An gudanar da bikin Maulidin Manzon Allah (S), Sayyida Zahra (SA) da Imam Ali (AS) a garin Potiskum da ke jihar Yobe, tare da raba kayan abinci ga al’umma.

Shaikh Abubakar Nuhu Talatar Mafara ne babban baƙon jawabi a wajen bikin Maulidin, yayin da Wakilin ’yan’uwa almajiran Shaikh Ibraheem Zakzaky na yankin Potiskum, Malam Ibrahim Lawan ya gabatar da shi ga mahalarta taron.

Bikin, wanda ɗan’uwa Alhaji Muhammad Adamu (Alhaji Baba) ya shirya, ya gudana ne a harabar gidansa da ke Potiskum daga ranar Laraba zuwa Juma’a, 7 zuwa 9 ga watan Janairu, 2026.

An fara taron ne da karatun Alƙur’ani mai girma (Musaffa) a ranar Laraba, inda aka kwana ana gudanar da karatun a ranar farko ta taron.

A ranar Alhamis kuwa, an gabatar da Majalisin Mawaƙa, tare da jawaban malamai, inda Shaikh Abdullahi Hassan da Shaikh Abubakar Muhammad Baba suka gabatar da nasu wa’azozin, suna masu jan hankalin al’umma kan koyarwar Ahlul Baiti (AS) da muhimmancin koyi da rayuwar Manzon Allah (S).

A ranar kammala taron, wato Juma’a, ɗalibi Sa’idu Saƙafa Potiskum ya gabatar da Majalisi. Haka kuma, an raba kyautuka na musamman ga mutum 24, tare da rabon kayan abinci da suka haɗa da ƙananan buhunan garin masara da shinkafa, wanda adadinsu ya kai buhu 548.

Jama’a sun bayyana jin daɗinsu matuƙa da wannan tagomshi da suka samu albarkacin zagayowar Maulidin tsarkakan bayi. Sun yi fatan alheri ga Jagoran Harkar Musulunci Shaikh Ibraheem Zakzaky da kuma wanda ya shirya taron Alhaji Muhammad Adamu.

Ga wasu daga cikin hotunan taron.

  • Related Posts

    Shugaban NASEMA, Akwash, Ya Bayyana Ayyukan Shekara Daya

    Daga Zubairu Lawal Babban Darakta Janar na NASEMA, Barrista Benjamin Akwash, ya gabatar da rahoton ayyukan shekara guda a Lafia, inda ya bayyana nasarori da kalubalen da hukumar ta fuskanta.…

    Karramawar Da Aka Yi Min Sakamakon Kyakkyawar Tarbiyya Ce Daga Iyayena -Amb. Dakta Nana Maryam Gwambe

    Daga Ibrahim Muhammad Kano Ƙungiyar WAZOBIA Conflicts Resolution and Peace Advocacy Initiative (WARCOPIA), ƙarƙashin jagorancin Ambasada Garba Sulaiman Marafa (Marafan Lagos), ta gudanar da taron karrama wasu zaɓaɓɓun mutane da…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Shugaban NASEMA, Akwash, Ya Bayyana Ayyukan Shekara Daya

    Shugaban NASEMA, Akwash, Ya Bayyana Ayyukan Shekara Daya

    Sanya Bukatun Kano A Gaba Zai Haɗa Kan Jama’a -Bala Muhammad Gwagwarwa

    Sanya Bukatun Kano A Gaba Zai Haɗa Kan Jama’a -Bala Muhammad Gwagwarwa

    ‘Ana Zargin Yunƙurin Ɓata Sunan Tsohon Mataimakin Gwamnan Kano’

    ‘Ana Zargin Yunƙurin Ɓata Sunan Tsohon Mataimakin Gwamnan Kano’

    Karramawar Da Aka Yi Min Sakamakon Kyakkyawar Tarbiyya Ce Daga Iyayena -Amb. Dakta Nana Maryam Gwambe

    Karramawar Da Aka Yi Min Sakamakon Kyakkyawar Tarbiyya Ce Daga Iyayena -Amb. Dakta Nana Maryam Gwambe

    DSS Ta Saki Jami’an Gwamnatin Kano Kan Zargin Ɓata Sunan Kwankwaso

    DSS Ta Saki Jami’an Gwamnatin Kano Kan Zargin Ɓata Sunan Kwankwaso

    HARIN TA’ADDANCI A BUKKUYUM: Gwamna Lawal Ya Bayyana Shi Da Aikin Rashin Imani

    HARIN TA’ADDANCI A BUKKUYUM: Gwamna Lawal Ya Bayyana Shi Da Aikin Rashin Imani