Hussaini Lili Gabari Ya Ziyarci Ado Tati Domin Neman Goyon Bayan APC a Dala

Daga Ibrahim Muhammad Kano

Mai neman tsayawa takarar kujerar Majalisar Jiha daga Ƙaramar Hukumar Dala, Hon. Hussaini Lili Gabari, ya kai ziyarar girmamawa ga jigon jam’iyyar APC, kuma shugaban jam’iyyar siyasa ta Gangariya na kasa, Hon. Ado Tati, domin neman hadin kai da goyon baya gabanin zaben 2027.

A yayin ziyarar, Lili Gabari ya bayyana cewa yana gudanar da wani rangaɗi ne na musamman ga masu ruwa da tsaki a jam’iyyar APC, domin gabatar da kansa tare da neman goyon bayansu.

Ya ce burinsa shi ne ganin jam’iyyar APC ta kasance cikin haɗin kai daga tushe har sama, domin tabbatar da nasara a zaɓuka masu zuwa.

Ya ƙara da cewa ba za a samu nasara ba sai an haɗa kan dukkan mambobin jam’iyyar, yana mai jaddada ƙudirinsa na yin aiki tare da kowa domin ƙarfafa jam’iyyar.

Da yake mayar da martani, Hon. Ado Tati ya bayyana cikakken goyon bayansa ga takarar Lili Gabari, inda ya siffanta shi a matsayin ɗan siyasa mai ƙwarewa, jajircewa, da manufofi masu amfani ga al’umma.

A cewarsa, “Ina da cikakken yaƙini cewa Lili Gabari ya cancanci ya wakilci al’ummar Dala a Majalisar Jiha. Ina tare da shi ɗari bisa ɗari.”

  • Related Posts

    An Yaba Da Wakilcin Hon. Sani Adamu Wakili A Ungogo Da Minjibir, An Nemi A Sake Tsayar Da Shi A 2027

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Al’ummar ƙananan hukumomin Ungogo da Minjibir a jihar kano sun bayyana gamsuwarsu da wakilcin da Hon. Sani Adamu Wakili ke yi musu a Majalisar Tarayya, tare…

    Sulhu Ya Samu: ATM Gwarzo Ya Janye Wa Barau A Takarar Sanata A APC Kano

    Daga Ibrahim Muhammad, Kano Jagoran Jam’iyyar APC a Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya jagoranci wani zama na sulhu da ya haɗa manyan jiga-jigan jam’iyyar biyu daga Kano ta Arewa,…

    Leave a Reply

    Your email address will not be published. Required fields are marked *

    You Missed

    Dan’iya mourns attack victims, urges decisive action against insecurity

    Dan’iya mourns attack victims, urges decisive action against insecurity

    Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

    Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

    BOMBOY: Nasarar Samun Tikitin Takara Ba Tare Da Hamayya Ba Ta Gwamna Abba Da Hassan Hussain Ta Nuna Gamsuwar Al’umma

    BOMBOY: Nasarar Samun Tikitin Takara Ba Tare Da Hamayya Ba Ta Gwamna Abba Da Hassan Hussain Ta Nuna Gamsuwar Al’umma

    Nasarar Atiku A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Na ADC, Nasara Ce Ga Masu Kishin Ci Gaban Ƙasa -Ambasada Mainasara Salga

    Nasarar Atiku A Matsayin Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa Na ADC, Nasara Ce Ga Masu Kishin Ci Gaban Ƙasa -Ambasada Mainasara Salga

    Gawuna Ya Zama Ɗan Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar NDC

    Gawuna Ya Zama Ɗan Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar NDC

    Sarkin Margunawan Kano Ya Taya Musulmi Murnar Sallah Ya Yi Kira Ga Kyautata Haɗin Kai Da Zaman Lafiya

    Sarkin Margunawan Kano Ya Taya Musulmi Murnar Sallah Ya Yi Kira Ga Kyautata Haɗin Kai Da Zaman Lafiya